Tsohon Shugaban karatu daga gida (Jami’ar National Open University of Nigeria), Farfesa Abdalla Uba Adamu, ya yi ritaya daga aiki a Jami’ar Bayero ta Kano bayan ya cika shekaru 70 a duniya. Ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Facebook a daren Juma’a.
Farfesan, wanda ke da muƙaman farfesa a fannonin Ilimin Kimiyya da kuma Sadarwa da Al’adu, ya ce ya shafe kusan shekaru 46 yana aiki a jami’ar, inda ya bayyana ta a matsayin gidansa. Ya ce ya fara aiki ne a ranar 24 ga Yuli, 1980 a matsayin mataimakin malami a sashin Ilimi, kafin daga bisani ya kammala aikinsa a sashin nazarin watsa labarai da sadarwa, wanda ya taimaka wajen kafa shi a 2014.
Da yake waiwaye kan rayuwarsa ta ilimi, Adamu ya ce tafiyar ta kasance mai wahala amma cike da nasara, yana mai cewa bai yi nadamar zaɓin da ya yi ba domin ya taimaka masa wajen zama mutum mafi nagarta. Ya kuma tuna yadda ya taɓa tattaunawa da mahaifinsa kan karantar likitanci, amma daga bisani ya tsinci kansa a fagen bincike wanda yake sha’awa.
Farfesan ya gode wa iyalansa, da abokan aiki da sauran abokan arziƙi bisa taimakon da suka ba shi tsawon shekarun aikinsa.
Ya kuma bayyana cewa ritaya ba ƙarshen aiki ba ne, domin zai ci gaba da gudanar da bincike da rubuce-rubuce, inda ya ce yana da wasu littattafai da dama da yake shirin kammalawa.















Discussion about this post