ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

by Rabi'u Ali Indabawa
2 months ago
Cafke

Rundunar ‘Yansandan Jihar Yobe ta kama wasu mutum bakwai da ake zargi mambobin wata kungiyar masu aikata laifuka, wadanda ake zargin suna da hannu a fasa gidaje, sata da kuma kwacen wayoyi a wasu sassan Damaturu, babban birnin jihar.

‘Yansanda sun ce an cafke wadanda ake zargin ne a wani samame na hadin gwiwa da jami’an sashen “A Dibision” na Damaturu suka gudanar tsakanin ranakun 16 zuwa 19 ga Afrilu, 2026.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar, SP Dungus Abdulkarim, ya fitar a ranar Talata.

ADVERTISEMENT

Abdulkarim ya ce samamen ya mayar da hankali ne kan ayyukan ta’addanci a yankunan Nayinawa, Bindigari, One Million Road da Pompomari.

Sanarwar ta ce: “Rundunar ‘Yansandan Jihar Yobe ta sake samun gagarumar nasara a kokarinta na yaki da laifuka da masu aikata su a fadin jihar.”

LABARAI MASU NASABA

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

Abdulkarim ya bayyana sunayen wadanda ake zargin da suka hada da Usman Mohd mai shekara (20), Abubakar Adamu mai shekara (20), Mohd Ibrahim mai shekara (22), Mohd Goni mai shekara (19), Khalifa Mohd (mai shekara 19), Abubakar Mohammed mai shekara (19), da Ali Mohammed mai shekara (23).

Ya kuma bayyana cewa wadanda ake zargin sun amsa aikata laifuka da dama yayin bincike.

“Yayin tambayoyi, sun amsa cewa suna da hannu a jerin laifukan fasa gidaje, sata da kwacen waya a yankunan da abin ya shafa,” in ji shi.

Kakakin ‘yansandan ya kara da cewa sun amince da satar wayoyin Android guda bakwai da kuma wayoyi na maballi guda biyu, inda aka riga aka kwato guda shida daga cikinsu.

“Sun amsa cewa sun sace wayoyin Android guda bakwai da kuma wayoyi biyu na maballi. An riga an kwato guda shida daga cikin wayoyin da aka sace,” in ji Abdulkarim.

Ya kara da cewa bincike na ci gaba, kuma za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu bayan kammala binciken.

“Bincike na gudana domin gurfanar da su yadda ya dace,” ya kara.

A wani bangare, Kwamishinan ‘Yansanda na jihar, Usman Kanfani Jibrin, ya yaba wa jami’an da suka gudanar da aikin, tare da bukatar su ci gaba da irin wannan kokari.

Sanarwar ta ce: “Kwamishinan ‘Yan Sanda ya yaba da kwarewa da jajircewar jami’an, tare da ba da umarnin ci gaba da gudanar da samame kan maboyar masu aikata laifuka a fadin jihar.”

Har ila yau, CP din ya jaddada muhimmancin amfani da bayanan sirri wajen aikin ‘yan sanda, tare da kira ga al’umma da su ci gaba da bai wa jami’an tsaro hadin kai.

“Ya jaddada bukatar kara sa ido da kuma amfani da bayanan sirri wajen aikin ‘yansanda, tare da rokon jama’a su ci gaba da bayar da sahihan bayanai domin taimakawa wajen yaki da laifuka,” in ji Abdulkarim.

A gefe guda kuma, Rundunar ‘Yansandan Jihar Ogun ta kama wasu mutum hudu da ake zargi ‘yan kungiyar asiri ne bisa zargin kai hari, fashi da makami da kuma mallakar bindiga ba bisa ka’ida ba.

An bayyana sunayen su da Samson John mai shekaru 25, Olufowora Michael mai shekaru 28, Odeh Samuel Ejeh mai shekaru 25, da Olajide Jeremiah mai shekaru 28.

Cafke
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Next Post
Rashin Ingantattun Cibiyoyin Kiwon Lafiya Da Talauci Ke Sa Al’umma Amfani Da Unguwarzoma Wajen Haihuwa A Yankunan Arewa

Rashin Ingantattun Cibiyoyin Kiwon Lafiya Da Talauci Ke Sa Al’umma Amfani Da Unguwarzoma Wajen Haihuwa A Yankunan Arewa

LABARAI MASU NASABA

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.