Rundunar ‘Yansandan Jihar Yobe ta kama wasu mutum bakwai da ake zargi mambobin wata kungiyar masu aikata laifuka, wadanda ake zargin suna da hannu a fasa gidaje, sata da kuma kwacen wayoyi a wasu sassan Damaturu, babban birnin jihar.
‘Yansanda sun ce an cafke wadanda ake zargin ne a wani samame na hadin gwiwa da jami’an sashen “A Dibision” na Damaturu suka gudanar tsakanin ranakun 16 zuwa 19 ga Afrilu, 2026.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar, SP Dungus Abdulkarim, ya fitar a ranar Talata.
Abdulkarim ya ce samamen ya mayar da hankali ne kan ayyukan ta’addanci a yankunan Nayinawa, Bindigari, One Million Road da Pompomari.
Sanarwar ta ce: “Rundunar ‘Yansandan Jihar Yobe ta sake samun gagarumar nasara a kokarinta na yaki da laifuka da masu aikata su a fadin jihar.”
Abdulkarim ya bayyana sunayen wadanda ake zargin da suka hada da Usman Mohd mai shekara (20), Abubakar Adamu mai shekara (20), Mohd Ibrahim mai shekara (22), Mohd Goni mai shekara (19), Khalifa Mohd (mai shekara 19), Abubakar Mohammed mai shekara (19), da Ali Mohammed mai shekara (23).
Ya kuma bayyana cewa wadanda ake zargin sun amsa aikata laifuka da dama yayin bincike.
“Yayin tambayoyi, sun amsa cewa suna da hannu a jerin laifukan fasa gidaje, sata da kwacen waya a yankunan da abin ya shafa,” in ji shi.
Kakakin ‘yansandan ya kara da cewa sun amince da satar wayoyin Android guda bakwai da kuma wayoyi na maballi guda biyu, inda aka riga aka kwato guda shida daga cikinsu.
“Sun amsa cewa sun sace wayoyin Android guda bakwai da kuma wayoyi biyu na maballi. An riga an kwato guda shida daga cikin wayoyin da aka sace,” in ji Abdulkarim.
Ya kara da cewa bincike na ci gaba, kuma za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu bayan kammala binciken.
“Bincike na gudana domin gurfanar da su yadda ya dace,” ya kara.
A wani bangare, Kwamishinan ‘Yansanda na jihar, Usman Kanfani Jibrin, ya yaba wa jami’an da suka gudanar da aikin, tare da bukatar su ci gaba da irin wannan kokari.
Sanarwar ta ce: “Kwamishinan ‘Yan Sanda ya yaba da kwarewa da jajircewar jami’an, tare da ba da umarnin ci gaba da gudanar da samame kan maboyar masu aikata laifuka a fadin jihar.”
Har ila yau, CP din ya jaddada muhimmancin amfani da bayanan sirri wajen aikin ‘yan sanda, tare da kira ga al’umma da su ci gaba da bai wa jami’an tsaro hadin kai.
“Ya jaddada bukatar kara sa ido da kuma amfani da bayanan sirri wajen aikin ‘yansanda, tare da rokon jama’a su ci gaba da bayar da sahihan bayanai domin taimakawa wajen yaki da laifuka,” in ji Abdulkarim.
A gefe guda kuma, Rundunar ‘Yansandan Jihar Ogun ta kama wasu mutum hudu da ake zargi ‘yan kungiyar asiri ne bisa zargin kai hari, fashi da makami da kuma mallakar bindiga ba bisa ka’ida ba.
An bayyana sunayen su da Samson John mai shekaru 25, Olufowora Michael mai shekaru 28, Odeh Samuel Ejeh mai shekaru 25, da Olajide Jeremiah mai shekaru 28.















Discussion about this post