ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

by Rabi'u Ali Indabawa
1 month ago
Cafke

Rundunar ‘Yansandan Jihar Yobe ta kama wasu mutum bakwai da ake zargi mambobin wata kungiyar masu aikata laifuka, wadanda ake zargin suna da hannu a fasa gidaje, sata da kuma kwacen wayoyi a wasu sassan Damaturu, babban birnin jihar.

‘Yansanda sun ce an cafke wadanda ake zargin ne a wani samame na hadin gwiwa da jami’an sashen “A Dibision” na Damaturu suka gudanar tsakanin ranakun 16 zuwa 19 ga Afrilu, 2026.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar, SP Dungus Abdulkarim, ya fitar a ranar Talata.

ADVERTISEMENT

Abdulkarim ya ce samamen ya mayar da hankali ne kan ayyukan ta’addanci a yankunan Nayinawa, Bindigari, One Million Road da Pompomari.

Sanarwar ta ce: “Rundunar ‘Yansandan Jihar Yobe ta sake samun gagarumar nasara a kokarinta na yaki da laifuka da masu aikata su a fadin jihar.”

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya

Abdulkarim ya bayyana sunayen wadanda ake zargin da suka hada da Usman Mohd mai shekara (20), Abubakar Adamu mai shekara (20), Mohd Ibrahim mai shekara (22), Mohd Goni mai shekara (19), Khalifa Mohd (mai shekara 19), Abubakar Mohammed mai shekara (19), da Ali Mohammed mai shekara (23).

Ya kuma bayyana cewa wadanda ake zargin sun amsa aikata laifuka da dama yayin bincike.

“Yayin tambayoyi, sun amsa cewa suna da hannu a jerin laifukan fasa gidaje, sata da kwacen waya a yankunan da abin ya shafa,” in ji shi.

Kakakin ‘yansandan ya kara da cewa sun amince da satar wayoyin Android guda bakwai da kuma wayoyi na maballi guda biyu, inda aka riga aka kwato guda shida daga cikinsu.

“Sun amsa cewa sun sace wayoyin Android guda bakwai da kuma wayoyi biyu na maballi. An riga an kwato guda shida daga cikin wayoyin da aka sace,” in ji Abdulkarim.

Ya kara da cewa bincike na ci gaba, kuma za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu bayan kammala binciken.

“Bincike na gudana domin gurfanar da su yadda ya dace,” ya kara.

A wani bangare, Kwamishinan ‘Yansanda na jihar, Usman Kanfani Jibrin, ya yaba wa jami’an da suka gudanar da aikin, tare da bukatar su ci gaba da irin wannan kokari.

Sanarwar ta ce: “Kwamishinan ‘Yan Sanda ya yaba da kwarewa da jajircewar jami’an, tare da ba da umarnin ci gaba da gudanar da samame kan maboyar masu aikata laifuka a fadin jihar.”

Har ila yau, CP din ya jaddada muhimmancin amfani da bayanan sirri wajen aikin ‘yan sanda, tare da kira ga al’umma da su ci gaba da bai wa jami’an tsaro hadin kai.

“Ya jaddada bukatar kara sa ido da kuma amfani da bayanan sirri wajen aikin ‘yansanda, tare da rokon jama’a su ci gaba da bayar da sahihan bayanai domin taimakawa wajen yaki da laifuka,” in ji Abdulkarim.

A gefe guda kuma, Rundunar ‘Yansandan Jihar Ogun ta kama wasu mutum hudu da ake zargi ‘yan kungiyar asiri ne bisa zargin kai hari, fashi da makami da kuma mallakar bindiga ba bisa ka’ida ba.

An bayyana sunayen su da Samson John mai shekaru 25, Olufowora Michael mai shekaru 28, Odeh Samuel Ejeh mai shekaru 25, da Olajide Jeremiah mai shekaru 28.

Cafke
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja
Kotu Da Ɗansanda

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

May 2, 2026
An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya

April 25, 2026
EFCC Ta Cafke Lauyan Bogi Da Mallakar Hatimin Kungiyar Lauyoyi Ta Nijeriya Na Jabu A Legas
Al'ajabi

EFCC Ta Cafke Lauyan Bogi Da Mallakar Hatimin Kungiyar Lauyoyi Ta Nijeriya Na Jabu A Legas

April 21, 2026
Next Post
Rashin Ingantattun Cibiyoyin Kiwon Lafiya Da Talauci Ke Sa Al’umma Amfani Da Unguwarzoma Wajen Haihuwa A Yankunan Arewa

Rashin Ingantattun Cibiyoyin Kiwon Lafiya Da Talauci Ke Sa Al’umma Amfani Da Unguwarzoma Wajen Haihuwa A Yankunan Arewa

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.