ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

by Rabi'u Ali Indabawa
3 months ago
Cafke

Rundunar ‘Yansandan Jihar Yobe ta kama wasu mutum bakwai da ake zargi mambobin wata kungiyar masu aikata laifuka, wadanda ake zargin suna da hannu a fasa gidaje, sata da kuma kwacen wayoyi a wasu sassan Damaturu, babban birnin jihar.

‘Yansanda sun ce an cafke wadanda ake zargin ne a wani samame na hadin gwiwa da jami’an sashen “A Dibision” na Damaturu suka gudanar tsakanin ranakun 16 zuwa 19 ga Afrilu, 2026.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar, SP Dungus Abdulkarim, ya fitar a ranar Talata.

ADVERTISEMENT

Abdulkarim ya ce samamen ya mayar da hankali ne kan ayyukan ta’addanci a yankunan Nayinawa, Bindigari, One Million Road da Pompomari.

Sanarwar ta ce: “Rundunar ‘Yansandan Jihar Yobe ta sake samun gagarumar nasara a kokarinta na yaki da laifuka da masu aikata su a fadin jihar.”

LABARAI MASU NASABA

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

Abdulkarim ya bayyana sunayen wadanda ake zargin da suka hada da Usman Mohd mai shekara (20), Abubakar Adamu mai shekara (20), Mohd Ibrahim mai shekara (22), Mohd Goni mai shekara (19), Khalifa Mohd (mai shekara 19), Abubakar Mohammed mai shekara (19), da Ali Mohammed mai shekara (23).

Ya kuma bayyana cewa wadanda ake zargin sun amsa aikata laifuka da dama yayin bincike.

“Yayin tambayoyi, sun amsa cewa suna da hannu a jerin laifukan fasa gidaje, sata da kwacen waya a yankunan da abin ya shafa,” in ji shi.

Kakakin ‘yansandan ya kara da cewa sun amince da satar wayoyin Android guda bakwai da kuma wayoyi na maballi guda biyu, inda aka riga aka kwato guda shida daga cikinsu.

“Sun amsa cewa sun sace wayoyin Android guda bakwai da kuma wayoyi biyu na maballi. An riga an kwato guda shida daga cikin wayoyin da aka sace,” in ji Abdulkarim.

Ya kara da cewa bincike na ci gaba, kuma za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu bayan kammala binciken.

“Bincike na gudana domin gurfanar da su yadda ya dace,” ya kara.

A wani bangare, Kwamishinan ‘Yansanda na jihar, Usman Kanfani Jibrin, ya yaba wa jami’an da suka gudanar da aikin, tare da bukatar su ci gaba da irin wannan kokari.

Sanarwar ta ce: “Kwamishinan ‘Yan Sanda ya yaba da kwarewa da jajircewar jami’an, tare da ba da umarnin ci gaba da gudanar da samame kan maboyar masu aikata laifuka a fadin jihar.”

Har ila yau, CP din ya jaddada muhimmancin amfani da bayanan sirri wajen aikin ‘yan sanda, tare da kira ga al’umma da su ci gaba da bai wa jami’an tsaro hadin kai.

“Ya jaddada bukatar kara sa ido da kuma amfani da bayanan sirri wajen aikin ‘yansanda, tare da rokon jama’a su ci gaba da bayar da sahihan bayanai domin taimakawa wajen yaki da laifuka,” in ji Abdulkarim.

A gefe guda kuma, Rundunar ‘Yansandan Jihar Ogun ta kama wasu mutum hudu da ake zargi ‘yan kungiyar asiri ne bisa zargin kai hari, fashi da makami da kuma mallakar bindiga ba bisa ka’ida ba.

An bayyana sunayen su da Samson John mai shekaru 25, Olufowora Michael mai shekaru 28, Odeh Samuel Ejeh mai shekaru 25, da Olajide Jeremiah mai shekaru 28.

Cafke
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Next Post
Rashin Ingantattun Cibiyoyin Kiwon Lafiya Da Talauci Ke Sa Al’umma Amfani Da Unguwarzoma Wajen Haihuwa A Yankunan Arewa

Rashin Ingantattun Cibiyoyin Kiwon Lafiya Da Talauci Ke Sa Al’umma Amfani Da Unguwarzoma Wajen Haihuwa A Yankunan Arewa

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.