• English
  • Business News
Monday, July 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fiye Da Mutum Miliyan 5 Ke Fuskantar Barazanar Kamuwa Da Cututtukan Yanayi Da Ake Watsi Da Su A Kaduna

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Fiye Da Mutum Miliyan 5 Ke Fuskantar Barazanar Kamuwa Da Cututtukan Yanayi Da Ake Watsi Da Su A Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamishinan lafiya ta jihar Kaduna, Umma K. Ahmed, ta bayyana cewa sama da mutane miliyan 5 a jihar na fuskantar barazanar kamuwa da cututtuka na yanayi da ake sakaci da su (NTDs) da suka hada da makanta da elephantiasis da dai sauransu.

Ta bayyana hakan ne a ranar Talata yayin da take ganawa da manema labarai domin bikin ranar yaki da cututtuka da ake sakaci da su, NTDs na duniya na shekarar 2024 a Kaduna.

  • Xi Ya Tayawa Azali Assoumani Murnar Sake Zaben Shugaban Comoros Ta Wayar Tarho
  • Micheal Keating: Kasar Sin Ba Barazanar Tattalin Arziki Ba Ce

A cewarta, Hukumar lafiya ta Duniya (WHO) ta kebe kowace ranar 30 ga watan Janairu, domin “fadakar da dukkan al’ummomin duniya kan illar NTDs, wanda ke shafar sama da mutane biliyan daya a fadin duniya, inda kusan kasashe 149 ke fuskantar wadannan cututtuka. kuma Afirka tana dauke da kusan rabin wannan cutar.”

“Nijeriya ita ce kasa ta biyu da ke da damuwa da illar NTDs a duniya, kuma itace a gaba wurin fama da barazanar cutar a Afirka da ke da mutane fiye da miliyan 120 da ke rayuwa a cikin hadarin kamuwa da cututtuka da ake sakaci ko watsi da su.

Cututtuka

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

“A jihar Kaduna, mutane 5,970,722 na fuskantar barazanar kamowa da cutar makanta, tsutsar ciki, filariasis lymphatic da bilharziasis” inji kwamishinar

Jihar Kaduna dai tana hada kai da duk masu ruwa da tsaki musamman kungiyoyin raya kasa masu zaman kansu (NGDOs) irin su Sightsavers, wajen bada goyon baya wurin magance matsalar NTDs a jihar Kaduna.

“Na yi matukar farin cikin bayar da rahoton cewa an samu gagarumin ci gaba cikin shekaru 10 da suka gabata, wanda hakan ya nuna mun samu nasarar dakile yaduwar cutar onchocerciasis a kananan hukumomi 16 da kuma kawar da cutar trachoma a jihar Kaduna, kamar yadda rahoton binciken cutar Trachoma ya nuna na 2023.

“Sauran nasarorin da ma’aikatar ta samu sun hada da kashe tsutsotsin ciki da ke barazana ga kananan yara da kuma raba Magungunan cutar Lymphatic Filariasis da Schistosomiasis masu yawa a fadin kananan hukumomi 23 na jihar.

“An horar da ma’aikatan kiwon lafiya 834 kan tantancewa da kula da cututtukan NTDs, an horar da malamai 3,502, da kuma mutane 10,249 don rarraba magunguna a tsakanin al’ummarsu a shekarar 2023.

“Ina so in sanar da ku duka cewa, jihar Kaduna ta himmatu wajen kara kaimi domin cimma burin hukumar kula da kiwon lafiya ta duniya na kawar da barazanar cutar NTDs nan da shekarar 2030 tare da ba da gudummawa ga ingantaccen tsarin kiwon lafiya ta hanyar inganta iya aiki, hada kan al’umma tare, da bayar da gudummawar kiwon lafiya na duniya baki daya.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaGwamnatin jihar KadunaKiwon Lafiya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Manufar Kasar Sin Daya Tak, Ra’Ayi Ne Dake Kara Tabbata Tsakanin Kasashen Duniya

Next Post

NDLEA Ta Cafke Masu Safarar Kwaya 198, Sun Lalata Wurin Sayar Da Kwaya 21 A Kano

Related

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato
Da ɗumi-ɗuminsa

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

5 hours ago
Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a
Labarai

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

6 hours ago
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson
Labarai

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

7 hours ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Ranar Talata Mai Zuwa Zan Koma Zauren Majalisar Dattawa – Sanata Natasha

10 hours ago
Za A Fara Sufurin Ma’aikata Da Ɗaliban Kaduna Kyauta A Bas
Labarai

Za A Fara Sufurin Ma’aikata Da Ɗaliban Kaduna Kyauta A Bas

13 hours ago
Mutane 8 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsari A Hanyar Lagos
Labarai

Mutane 8 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsari A Hanyar Lagos

14 hours ago
Next Post
NDLEA Ta Cafke Masu Safarar Kwaya 198, Sun Lalata Wurin Sayar Da Kwaya 21 A Kano

NDLEA Ta Cafke Masu Safarar Kwaya 198, Sun Lalata Wurin Sayar Da Kwaya 21 A Kano

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

July 6, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

July 6, 2025
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

July 6, 2025
Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

July 6, 2025
Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

July 6, 2025
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

July 6, 2025
Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

July 6, 2025
Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

July 6, 2025
Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

July 6, 2025
Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

July 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.