ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fiye Da Mutum Miliyan 5 Ke Fuskantar Barazanar Kamuwa Da Cututtukan Yanayi Da Ake Watsi Da Su A Kaduna

by Sulaiman
3 years ago
Cututtuka

Kwamishinan lafiya ta jihar Kaduna, Umma K. Ahmed, ta bayyana cewa sama da mutane miliyan 5 a jihar na fuskantar barazanar kamuwa da cututtuka na yanayi da ake sakaci da su (NTDs) da suka hada da makanta da elephantiasis da dai sauransu.

Ta bayyana hakan ne a ranar Talata yayin da take ganawa da manema labarai domin bikin ranar yaki da cututtuka da ake sakaci da su, NTDs na duniya na shekarar 2024 a Kaduna.

  • Xi Ya Tayawa Azali Assoumani Murnar Sake Zaben Shugaban Comoros Ta Wayar Tarho
  • Micheal Keating: Kasar Sin Ba Barazanar Tattalin Arziki Ba Ce

A cewarta, Hukumar lafiya ta Duniya (WHO) ta kebe kowace ranar 30 ga watan Janairu, domin “fadakar da dukkan al’ummomin duniya kan illar NTDs, wanda ke shafar sama da mutane biliyan daya a fadin duniya, inda kusan kasashe 149 ke fuskantar wadannan cututtuka. kuma Afirka tana dauke da kusan rabin wannan cutar.”

ADVERTISEMENT

“Nijeriya ita ce kasa ta biyu da ke da damuwa da illar NTDs a duniya, kuma itace a gaba wurin fama da barazanar cutar a Afirka da ke da mutane fiye da miliyan 120 da ke rayuwa a cikin hadarin kamuwa da cututtuka da ake sakaci ko watsi da su.

Cututtuka

LABARAI MASU NASABA

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

“A jihar Kaduna, mutane 5,970,722 na fuskantar barazanar kamowa da cutar makanta, tsutsar ciki, filariasis lymphatic da bilharziasis” inji kwamishinar

Jihar Kaduna dai tana hada kai da duk masu ruwa da tsaki musamman kungiyoyin raya kasa masu zaman kansu (NGDOs) irin su Sightsavers, wajen bada goyon baya wurin magance matsalar NTDs a jihar Kaduna.

“Na yi matukar farin cikin bayar da rahoton cewa an samu gagarumin ci gaba cikin shekaru 10 da suka gabata, wanda hakan ya nuna mun samu nasarar dakile yaduwar cutar onchocerciasis a kananan hukumomi 16 da kuma kawar da cutar trachoma a jihar Kaduna, kamar yadda rahoton binciken cutar Trachoma ya nuna na 2023.

“Sauran nasarorin da ma’aikatar ta samu sun hada da kashe tsutsotsin ciki da ke barazana ga kananan yara da kuma raba Magungunan cutar Lymphatic Filariasis da Schistosomiasis masu yawa a fadin kananan hukumomi 23 na jihar.

“An horar da ma’aikatan kiwon lafiya 834 kan tantancewa da kula da cututtukan NTDs, an horar da malamai 3,502, da kuma mutane 10,249 don rarraba magunguna a tsakanin al’ummarsu a shekarar 2023.

“Ina so in sanar da ku duka cewa, jihar Kaduna ta himmatu wajen kara kaimi domin cimma burin hukumar kula da kiwon lafiya ta duniya na kawar da barazanar cutar NTDs nan da shekarar 2030 tare da ba da gudummawa ga ingantaccen tsarin kiwon lafiya ta hanyar inganta iya aiki, hada kan al’umma tare, da bayar da gudummawar kiwon lafiya na duniya baki daya.”

Cututtuka
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan
  • Sulaiman
    ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

MASU ALAKA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Next Post
NDLEA Ta Cafke Masu Safarar Kwaya 198, Sun Lalata Wurin Sayar Da Kwaya 21 A Kano

NDLEA Ta Cafke Masu Safarar Kwaya 198, Sun Lalata Wurin Sayar Da Kwaya 21 A Kano

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.