• English
  • Business News
Tuesday, July 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fiye Da Mutum Miliyan 5 Ke Fuskantar Barazanar Kamuwa Da Cututtukan Yanayi Da Ake Watsi Da Su A Kaduna

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Fiye Da Mutum Miliyan 5 Ke Fuskantar Barazanar Kamuwa Da Cututtukan Yanayi Da Ake Watsi Da Su A Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamishinan lafiya ta jihar Kaduna, Umma K. Ahmed, ta bayyana cewa sama da mutane miliyan 5 a jihar na fuskantar barazanar kamuwa da cututtuka na yanayi da ake sakaci da su (NTDs) da suka hada da makanta da elephantiasis da dai sauransu.

Ta bayyana hakan ne a ranar Talata yayin da take ganawa da manema labarai domin bikin ranar yaki da cututtuka da ake sakaci da su, NTDs na duniya na shekarar 2024 a Kaduna.

  • Xi Ya Tayawa Azali Assoumani Murnar Sake Zaben Shugaban Comoros Ta Wayar Tarho
  • Micheal Keating: Kasar Sin Ba Barazanar Tattalin Arziki Ba Ce

A cewarta, Hukumar lafiya ta Duniya (WHO) ta kebe kowace ranar 30 ga watan Janairu, domin “fadakar da dukkan al’ummomin duniya kan illar NTDs, wanda ke shafar sama da mutane biliyan daya a fadin duniya, inda kusan kasashe 149 ke fuskantar wadannan cututtuka. kuma Afirka tana dauke da kusan rabin wannan cutar.”

“Nijeriya ita ce kasa ta biyu da ke da damuwa da illar NTDs a duniya, kuma itace a gaba wurin fama da barazanar cutar a Afirka da ke da mutane fiye da miliyan 120 da ke rayuwa a cikin hadarin kamuwa da cututtuka da ake sakaci ko watsi da su.

Cututtuka

Labarai Masu Nasaba

ADC: Tinubu Na Yunƙurin Raba Kawunan Masu Haɗaka Kafin Zaɓen 2027

Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima

“A jihar Kaduna, mutane 5,970,722 na fuskantar barazanar kamowa da cutar makanta, tsutsar ciki, filariasis lymphatic da bilharziasis” inji kwamishinar

Jihar Kaduna dai tana hada kai da duk masu ruwa da tsaki musamman kungiyoyin raya kasa masu zaman kansu (NGDOs) irin su Sightsavers, wajen bada goyon baya wurin magance matsalar NTDs a jihar Kaduna.

“Na yi matukar farin cikin bayar da rahoton cewa an samu gagarumin ci gaba cikin shekaru 10 da suka gabata, wanda hakan ya nuna mun samu nasarar dakile yaduwar cutar onchocerciasis a kananan hukumomi 16 da kuma kawar da cutar trachoma a jihar Kaduna, kamar yadda rahoton binciken cutar Trachoma ya nuna na 2023.

“Sauran nasarorin da ma’aikatar ta samu sun hada da kashe tsutsotsin ciki da ke barazana ga kananan yara da kuma raba Magungunan cutar Lymphatic Filariasis da Schistosomiasis masu yawa a fadin kananan hukumomi 23 na jihar.

“An horar da ma’aikatan kiwon lafiya 834 kan tantancewa da kula da cututtukan NTDs, an horar da malamai 3,502, da kuma mutane 10,249 don rarraba magunguna a tsakanin al’ummarsu a shekarar 2023.

“Ina so in sanar da ku duka cewa, jihar Kaduna ta himmatu wajen kara kaimi domin cimma burin hukumar kula da kiwon lafiya ta duniya na kawar da barazanar cutar NTDs nan da shekarar 2030 tare da ba da gudummawa ga ingantaccen tsarin kiwon lafiya ta hanyar inganta iya aiki, hada kan al’umma tare, da bayar da gudummawar kiwon lafiya na duniya baki daya.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaGwamnatin jihar KadunaKiwon Lafiya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Manufar Kasar Sin Daya Tak, Ra’Ayi Ne Dake Kara Tabbata Tsakanin Kasashen Duniya

Next Post

NDLEA Ta Cafke Masu Safarar Kwaya 198, Sun Lalata Wurin Sayar Da Kwaya 21 A Kano

Related

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

ADC: Tinubu Na Yunƙurin Raba Kawunan Masu Haɗaka Kafin Zaɓen 2027

35 minutes ago
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Manyan Labarai

Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima

2 hours ago
Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC
Labarai

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

11 hours ago
NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19
Da ɗumi-ɗuminsa

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

12 hours ago
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista
Da ɗumi-ɗuminsa

Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

13 hours ago
Gwamna Peter Mbah Ya Ƙaddamar Da Jiragen Kasuwanci 3 Na ‘Enugu Air’ Mallakin Jihar
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Peter Mbah Ya Ƙaddamar Da Jiragen Kasuwanci 3 Na ‘Enugu Air’ Mallakin Jihar

14 hours ago
Next Post
NDLEA Ta Cafke Masu Safarar Kwaya 198, Sun Lalata Wurin Sayar Da Kwaya 21 A Kano

NDLEA Ta Cafke Masu Safarar Kwaya 198, Sun Lalata Wurin Sayar Da Kwaya 21 A Kano

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

ADC: Tinubu Na Yunƙurin Raba Kawunan Masu Haɗaka Kafin Zaɓen 2027

July 8, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima

July 8, 2025
Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

July 7, 2025
Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

July 7, 2025
Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

July 7, 2025
Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

July 7, 2025
NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

July 7, 2025
Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

July 7, 2025
Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan

Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan

July 7, 2025
Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

July 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.