ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fiye Da Mutum Miliyan 5 Ke Fuskantar Barazanar Kamuwa Da Cututtukan Yanayi Da Ake Watsi Da Su A Kaduna

by Sulaiman
2 years ago
Cututtuka

Kwamishinan lafiya ta jihar Kaduna, Umma K. Ahmed, ta bayyana cewa sama da mutane miliyan 5 a jihar na fuskantar barazanar kamuwa da cututtuka na yanayi da ake sakaci da su (NTDs) da suka hada da makanta da elephantiasis da dai sauransu.

Ta bayyana hakan ne a ranar Talata yayin da take ganawa da manema labarai domin bikin ranar yaki da cututtuka da ake sakaci da su, NTDs na duniya na shekarar 2024 a Kaduna.

  • Xi Ya Tayawa Azali Assoumani Murnar Sake Zaben Shugaban Comoros Ta Wayar Tarho
  • Micheal Keating: Kasar Sin Ba Barazanar Tattalin Arziki Ba Ce

A cewarta, Hukumar lafiya ta Duniya (WHO) ta kebe kowace ranar 30 ga watan Janairu, domin “fadakar da dukkan al’ummomin duniya kan illar NTDs, wanda ke shafar sama da mutane biliyan daya a fadin duniya, inda kusan kasashe 149 ke fuskantar wadannan cututtuka. kuma Afirka tana dauke da kusan rabin wannan cutar.”

ADVERTISEMENT

“Nijeriya ita ce kasa ta biyu da ke da damuwa da illar NTDs a duniya, kuma itace a gaba wurin fama da barazanar cutar a Afirka da ke da mutane fiye da miliyan 120 da ke rayuwa a cikin hadarin kamuwa da cututtuka da ake sakaci ko watsi da su.

Cututtuka

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

“A jihar Kaduna, mutane 5,970,722 na fuskantar barazanar kamowa da cutar makanta, tsutsar ciki, filariasis lymphatic da bilharziasis” inji kwamishinar

Jihar Kaduna dai tana hada kai da duk masu ruwa da tsaki musamman kungiyoyin raya kasa masu zaman kansu (NGDOs) irin su Sightsavers, wajen bada goyon baya wurin magance matsalar NTDs a jihar Kaduna.

“Na yi matukar farin cikin bayar da rahoton cewa an samu gagarumin ci gaba cikin shekaru 10 da suka gabata, wanda hakan ya nuna mun samu nasarar dakile yaduwar cutar onchocerciasis a kananan hukumomi 16 da kuma kawar da cutar trachoma a jihar Kaduna, kamar yadda rahoton binciken cutar Trachoma ya nuna na 2023.

“Sauran nasarorin da ma’aikatar ta samu sun hada da kashe tsutsotsin ciki da ke barazana ga kananan yara da kuma raba Magungunan cutar Lymphatic Filariasis da Schistosomiasis masu yawa a fadin kananan hukumomi 23 na jihar.

“An horar da ma’aikatan kiwon lafiya 834 kan tantancewa da kula da cututtukan NTDs, an horar da malamai 3,502, da kuma mutane 10,249 don rarraba magunguna a tsakanin al’ummarsu a shekarar 2023.

“Ina so in sanar da ku duka cewa, jihar Kaduna ta himmatu wajen kara kaimi domin cimma burin hukumar kula da kiwon lafiya ta duniya na kawar da barazanar cutar NTDs nan da shekarar 2030 tare da ba da gudummawa ga ingantaccen tsarin kiwon lafiya ta hanyar inganta iya aiki, hada kan al’umma tare, da bayar da gudummawar kiwon lafiya na duniya baki daya.”

Cututtuka
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
  • Sulaiman
    Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari
  • Sulaiman
    Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

MASU ALAKA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Rahotonni

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Next Post
NDLEA Ta Cafke Masu Safarar Kwaya 198, Sun Lalata Wurin Sayar Da Kwaya 21 A Kano

NDLEA Ta Cafke Masu Safarar Kwaya 198, Sun Lalata Wurin Sayar Da Kwaya 21 A Kano

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.