Sanarwar baya bayan nan ta tsagaita bude wuta mai wa’adin makonni biyu tsakanin Amurka da Iran wadda kuma Israila ta goyi baya, ta faranta ran sassan kasa da kasa, ko da yake hakan ba ya nuni ga kawo karshen yankin baki daya. Illa dai mataki ne mai matukar muhimmanci na sassauta mummunan yanayin da aka shiga.
Al’ummun duniya sun shaida makonni na dauki ba dadi, da tattaunawar bayan fage tsakanin wasu sassa, da matsin lamba daga sassan kasa da kasa, bayan tafka asarar rayuka da lalata tarin ababen more rayuwa. Kazalika, an ga yadda kasuwar albarkatun mai ta shiga wani hali na matsi, bayan katsewar hanyar sufurin danyen mai ta mashigin Hormuz, wanda hakan ya yi mummunan tasiri ga tattalin arzikin duniya baki daya.
A takaice, dukkanin kasashen duniya sun dandana mummunan tasirin wannan yaki, sun kuma kara fahimtar muhimmancin kaucewa ci gabansa, da ma matukar bukatar kawo karshensa baki daya.
Masharhanta da dama na cewa, tun asali ma bai kamata a tsunduma cikin wannan yaki ba, wato dai kasashen da suka jawo barkewarsa sun zabi yin hakan ne bisa radin kansu, ba wai domin ya zama wajibi ba. Kuma ba su yi la’akari da muradun sauran kasashen duniya ba. Hakan ne ma ya sa kasashen da suka shige gaba, wajen ganin an cimma matsayar tsagaita wutar yakin, kamar Sin da Pakistan da suka gabatar da shawarwarin cimma wannan buri, suka sha nanata haramcin kaddamar da yaki ba tare da amincewar kwamitin tsaron MDD ba.
Muna iya cewa wannan mataki na dakatar da bude wuta na makonni biyu, wata dama ce aka samu ta komawa ga diflomasiyya. To sai dai kuma akwai masu ganin cewa da wuya Iran ta saki jiki da matakin, duba da cewa a baya ana tsaka da tattaunawa ne aka fara kaddamar da hare-hare kan yankunanta. Hakan ya sa matakan da za mu gani a yanzu ke da matukar muhimmanci, wajen tabbatar da ko dakatar da bude wutar zai haifar da matakan din din din na kawo karshen yakin ko kuwa a’a.
Amma a bangaren akasarin kasashen duniya masu fatan ganin an kawo karshen wannan yaki baki daya, burinsu shi ne tsagaita wutar na yanzu ya kai ga samar da dama ta cimma cikakkiyar yarjejeniya. Sassan kasa da kasa na da burin ganin bayan wannan yaki baki daya, tare da fatan hana maimaituwarsa a nan gaba. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post