• English
  • Business News
Saturday, August 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Garambawul Da Muke Wa Tsarin Aikin Sojojin Nijeriya –Janar Musa

by Sadiq
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Garambawul Da Muke Wa Tsarin Aikin Sojojin Nijeriya –Janar Musa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban Hafsan Hafsoshin Sojojin Nijeriya, Janar Christopher Musa ya bayyana yadda a halin yanzu rundunar sojin Nijeriya take kokarin samar da walwala ga jami’anta domin dawo da su hayyacinsu da kuma yin garambawul a aikin soji.

Janar din ya bayyana haka ne a wata ganawa da manema labarai da ya yi a ofishinsa kwanan baya. Mun yi nazarin bidiyon tattaunawar daga kafar yada labarai ta DW.

  • Sin Na Goyon Bayan Kokarin Kasashen Afrika Na Magance Matsaloli Ta Hanyar Da Suka Zaba
  • Nijeriya Ta Koma Matsayi Na 38 A Kasashen Da Suka Fi Iya Taka Leda A Duniya

Da aka tambaye shi irin sauyin da ya kawo tun lokacin da aka nada shi shugaban rundunonin sojin ruwa da sama da na kasa. Ya bayyana cewa, tun kafin zuwa wannan lokaci ya zauna a Maiduguri wajen watanni 19, “inda Allah ya taimake mu muka yi aiki a can kuma muka samar da hadin kan jama’a, kuma muka nusar da al’umma cewa kowa yana da aikin da ya kamata ya yi domin kawo zaman lafiya, kowa akwai gudunmawar da ya kamata ya rika kawowa, domin shi wannan aiki mu kadai ba za mu iya yi ba sai da taimakon jama’a, kuma yin hakan yana taimako sosai, shi ya sa a yanzu abubuwa suke canjawa.

 “Baya ga hakan, muna hulda da jama’a ba wai zaman ofis kawai muke yi ba muna fita waje muna hada kai da mutane da sauran ma’aikatu, muna gaya musu cewa ya kamata su ma su taimaka, domin duk wanda ya zo muka yi aiki tare muna yi ne don mu samu nasara,” in ji shi.

Da yake magana game da tsarin kula da walwalar sojojin da suke filin daga kuwa, Janar Musa ya ce, “Eh, mun sani cewa, idan soja ya ji dadin aikin da yake yi kuma yana samun abinci, albashinsa na zuwa ana taimakon iyalinsa da komai, to zai sa kwazo sosai domin ya samu nasara. To matakin dai da muka dauka yanzu shi ne, wadanda suka samu rauni a filin daga ana kai su asibiti ana lura da su yadda ya kamata, wadanda ma abin ya yi kamari ana kai su kasashen waje don su samu kulawa, wadanda kuma suka mutu ana tabbatar da cewa abubuwan da ya kamata a ba su na hakkinsu ana ba su, matansu gwamnati tana kula da su domin sun rasa mazajensu.”

Labarai Masu Nasaba

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

Da ya koma kan batun kokarin da gwamnatin Shugaba Tinubu ke yi na samar da alawus din sojoji kuwa, cewa ya yi, “To na farko dai abin da ake ciki mun dai tabbatar cewa kowa yana samun albashinsa yadda ya kamata, alawus dinsa yana samuwa, kayayyakin da yake bukata na aiki da na sawa ana bayarwa. Eh, babu shakka kudin bai da yawa ba ya isa amma muna roka a kara musu kuma shi shugaban kasa ya yarda cewa gaskiya ya kamata a kara kuma ana kan aiki, ka san ba abin da za a yi a kwana daya ba ne, to abubuwan suna tafiya kuma sojojinmu suna aiki tsakaninsu da Allah kuma suna cewa shi shugaban kasa yana tare da su.”

Da ya zo magana kan sojojin da ake bari a filin daga na tsawon lokaci ba tare da sun ga iyalinsu ba, Janar Christopher Musa ya bayyana cewa, a halin yanzu suna tabbatar da kowane soja yana samun damar ya je ya ga iyalinsa ya dawo ta hanyar ba da ‘Pass’, sannan kuma bayan shekara daya ko shekara biyu ana canja su gaba daya, duk inda suke aiki ma ana samu a canja su kuma ana ba su lokaci su je su ga iyalinsu.

“Mu ma mun san cewa idan soja ya zauna bai ga iyali ba yana damuwa ba zai yi aiki yadda ya kamata ba, wannan abu ne da muka dauke shi da muhimmanci.

A can Borno muna da jirgin sama da yake daukar su sati bibiyu su je hutu su dawo, sannan haka muke yi a sauran wurare don aiki ya ci gaba,” in ji shi.

Ya ci gaba da cewa, a kowane wata ana daukar sunaye, “mun san lokacin da ka zo don ba mu so ka dade da yawa, to abin da muke yi kenan kuma mun tabbatar da wannan tsarin yana aiki sosai.”

Dangane da batun hakkin sojojin da suka rasa rayukansu da aka ce aka rikewa kuwa, cewa ya yi “ai wannan a da kenan, amma a yanzu da zarar abin ya faru ake daukar mataki, za mu tabbatar sun samu hakkinsu don ba mu son su sha wahala.

“Ka ga wadanda suke da rai suna kallon wadanda suka rasu, idan ba su ga ana kyauta musu ba to babu wanda zai ba da kuzari wajen aiki. Wadanda suka rasu kwanaki da shugaban kasa ya je wajen jana’izarsu ka ga yadda ya ba wa ‘ya’yansu tallafin karatu ya kuma tabbatar da cewa za a biya su kudinsu tare da ba su gidaje, to abubuwanda ake yi kenan domin a tabbatar da cewa kasa na tare da su ba wanda za a manta da shi wai don ya rasu.

“Amma dama abin da muka gane shi ne, biyan alawus dinsu yana daukar lokaci, sai ka ga an yi shekara da shekaru ba a biya ba, amma mun yi magana da shugaban kasa yanzu ma ya ba da kudi ya ce a biya kowa gaba daya, to a halin yanzu abin da ake kan yi kenan za a biya su, ba ma son ana rike kudin kowa.”

A karshe ya ja hankalin masu aikata miyagun laifuka da ke kawo barazana ga zaman lafiyar kasa musamman ‘yan ta’adda da masu kai musu bayanai cewa su shiga taitayinsu.

“Abin da nake so na roki jama’a shi ne, mu sani wannan kasa da Allah ya ba mu kasa kuma mai albarka, dukkanmu mu hada kanmu domin ganin wannan kasar ta ci gaba, babu wanda zai iya wannan aiki shi kadai ko jami’an tsaro ko ‘yan siyasa dukkanmu ‘yan Nijeriya ya kamata mu kama aikin a yi tare, mu roki Allah, mu zauna mu tabbatar da cewa wannan kasa tamu ta ci gaba kuma tare ne za mu iya yi babu wanda zai iya yi shi kadai, kuma a bar hulda da ‘yan ta’adda, don muna da matsala da wadanda suke gaya musu ga sojoji nan, ga motoci nan, kaza-kaza-kaza, duk a bar wannan. Amma abin da nake fada a nan shi ne, abokin barawo barawo ne, mai aiki da ‘yan ta’adda shi ma dan ta’adda ne.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Aikin SojaGarambawulJanar Musa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ya Kamata A Karfafa Manufar Amfani Da Harsunan Gado A Makarantu

Next Post

Abin Da Ke Dagula Rashin Tsaron Nijeriya – Babban Hafsan Sojin Sama

Related

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 
Da ɗumi-ɗuminsa

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

3 hours ago
Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO
Manyan Labarai

Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

4 hours ago
Yarjejeniyar Dala Biliyan Ɗaya Da Ƙasar Brazil Za Ta Haɓaka Fannin Noma A Nijeriya —Tinubu
Manyan Labarai

Yarjejeniyar Dala Biliyan Ɗaya Da Ƙasar Brazil Za Ta Haɓaka Fannin Noma A Nijeriya —Tinubu

10 hours ago
ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye
Manyan Labarai

ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye

11 hours ago
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

23 hours ago
An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano
Manyan Labarai

An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano

1 day ago
Next Post
Abin Da Ke Dagula Rashin Tsaron Nijeriya – Babban Hafsan Sojin Sama

Abin Da Ke Dagula Rashin Tsaron Nijeriya - Babban Hafsan Sojin Sama

LABARAI MASU NASABA

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

August 2, 2025
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

August 2, 2025
Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

August 2, 2025
Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

August 2, 2025
An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

August 2, 2025
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

August 2, 2025
Gwamna Fintiri Ya Karrama Kocin Super Falcons, Madugu Da Naira Miliyan 50

Gwamna Fintiri Ya Karrama Kocin Super Falcons, Madugu Da Naira Miliyan 50

August 2, 2025
Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

August 2, 2025
Sauya Sheƙa: Sanatoci Biyu APC Ke Buƙata Wajen Samun Kashi Biyu Cikin Uku A Majalisar Dattawa

Sauya Sheƙa: Sanatoci Biyu APC Ke Buƙata Wajen Samun Kashi Biyu Cikin Uku A Majalisar Dattawa

August 2, 2025
An Sake Kashe Wata Ɗalibar Jami’ar Ondo

An Sake Kashe Wata Ɗalibar Jami’ar Ondo

August 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.