Rundunar ‘Yansandan Nijeriya ta fitar da gargadin tsaro a faɗin ƙasar kan yiwuwar kai hare-haren ta’addanci a makarantu, wuraren ibada, sansanonin horas da matasa na NYSC da sauran wuraren tarukan al’umma.
Gargadin ya biyo bayan bayanan sirri da suka nuna cewa wasu ‘yan ta’adda na shirin gudanar da hare-hare a sassa daban-daban na ƙasar, musamman yankunan Arewa maso Gabas, Arewa maso Yamma, Arewa ta Tsakiya da wasu sassan Kudu maso Yamma.
Rundunar ta kuma bayyana damuwa kan rahotannin motsin wasu ‘yan bindiga dauke da makamai daga Katsina ta Kaduna zuwa Jihar Filato, yayin da ake zargin wasu ‘yan ISWAP da masu haɗin gwiwarsu na gudanar da sa ido kan wuraren da za su iya kai hari.
‘Yansandan sun ce makarantu na cikin wuraren da suka fi fuskantar barazana, musamman yayin da ake shirin komawa karatu a zangon shekarar 2026/2027, inda ‘yan ta’adda za su iya amfani da cunkoson ɗalibai da malamai wajen haddasa asarar rayuka masu yawa.
Bayanin sirrin ya kuma nuna yiwuwar kai hare-hare gabanin babban zaɓen 2027, da nufin haifar da tsoro da dagula zaman lafiyar al’umma.
Saboda haka, Rundunar ta umarci kwamandojin ‘yansanda da su ƙara sa ido da sintiri, binciken ababen hawa da mutane, tare da tsaurara matakan tsaro a makarantu, wuraren ibada, sansanonin NYSC da sauran wurare masu muhimmanci.
Ta kuma bukaci a ƙarfafa jami’an kai agajin gaggawa tare da tsaurara tsaro a kan iyakokin jihohi, hanyoyin shiga da fita da sauran muhimman hanyoyin da ‘yan ta’adda za su iya amfani da su.














