Dubban mutane da wata mummunar girgizar ƙasa ta raba da muhallansu a gabashin Indonesia sun kwana a makarantu, ofisoshin ‘yansanda da gine-ginen gwamnati, yayin da suke jiran agajin gaggawa.
Girgizar ƙasar mai ƙarfin makin 7.7 ta afku da sanyin safiyar Asabar, inda ta kashe mutane 54 tare da jikkata fiye da 100. Jami’an ceto sun ce har yanzu ba a samu rahoton wasu mutane da suka ɓace ba.
Mai magana da yawun Hukumar Kula da Bala’o’i ta Ƙasa ta Indonesia (BNPB), Berton Suar Pelita Panjaitan, ya shaida wa AFP cewa zuwa safiyar Litinin, adadin mutanen da suka kasa komawa gidajensu ya kai 12,800, waɗanda suka bazu a garuruwa da dama da ke tsibirin Flores.
Hukumar kula da yanayin ƙasa ta Indonesia (BMKG) ta ce an samu ƙananan girgizar ƙasa sama da 1,600 bayan babbar girgizar, lamarin da ya sa mazauna yankin da dama suka ji tsoron komawa gidajensu.Rahotanni sun ce mazauna Flores da dama na shirin sake kwana a waje karo na uku, saboda fargabar sake faruwar girgizar ƙasa.














