ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Kafa Tarihi, Yayin Da Aka Fara Jigilar Alhazai Daga Filin Jirgin Sama Na Gusau

by Sulaiman
3 weeks ago
Lawal

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya kafa sabon tarihi bayan da aka gudanar da jigilar farko na aikin Hajji daga Filin Jirgin Sama na Ƙasa da Ƙasa da ke Gusau.

Jirgin Hajjin na farko ya tashi ne daga filin jirgin ranar Juma’a ɗauke da maniyyata 415 na jihar Zamfara a jirgin kamfanin Max Air mai lamba NGL270 zuwa ƙasar Saudiyya domin gudanar da aikin Hajjin bana.

Rahotanni sun nuna cewa daga cikin maniyyatan akwai maza 288 da mata 127.Da yake jawabi yayin ƙaddamar da tashin jirgin, Gwamna Lawal ya bayyana farin cikin sa da godiyar sa bisa ganin wannan gagarumin ci gaba da ya ce zai kasance abin tarihi a jihar Zamfara.Gwamnan ya bayyana gina Filin Jirgin Sama na Ƙasa da Ƙasa na Gusau a matsayin ɗaya daga cikin manyan ayyukan tarihi da gwamnatin sa ta sa a gaba, kuma alhamdu lillahi, ta cimma nasara.

ADVERTISEMENT

“Ina farin ciki matuƙa a yau ganin maniyyatan mu suna tashi kai tsaye daga Filin Jirgin Sama na Gusau zuwa ƙasar Saudiyya domin aikin Hajjin bana,” in ji gwamnan.

Ya ƙara da cewa, mutane da dama sun yi shakku kan yiwuwar aikin ya zama gaskiya, amma yanzu an tabbatar da hakan bayan an fara aikin gina filin jirgin tun ranar 18 ga watan Yunin 2024.

LABARAI MASU NASABA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

“Ba zan iya bayyana irin farin cikin da nake ciki ba. Wannan babbar dama ce ga maniyyatanmu domin tafiya cikin sauƙi da kwanciyar hankali. Cikin ƙasa da awa huɗu za su isa Saudiyya. A baya kuwa sai sun je Kano ko Sakkwato kafin su samu jirgin Hajji,” in ji gwamnan.

Gwamnan ya ce, wannan nasara wata babban mataki ne na tarihi tare da cika ɗaya daga cikin alƙawuran da ya ɗauka a lokacin yaƙin neman zaɓe.“Wannan tarihi ne mai girma kuma cikar alƙawarin da muka yi wa al’umma. Ina da ƙudurin ci gaba da aiwatar da ayyukan ci gaba domin jihar mu,” in ji shi.

Ya gode wa al’ummar jihar bisa addu’o’insu da kuma amincewar da suka nuna ga gwamnatinsa, yana mai cewa wannan shi ne farkon wasu manyan nasarori.Haka kuma gwamnan ya bayyana cewa gwamnatin jihar ta fara tattaunawa da kamfanonin jiragen sama domin fara zirga-zirgar kasuwanci daga Filin Jirgin Sama na Gusau nan gaba.

A ƙarshe, ya yi wa maniyyatan fatan sauka lafiya da gudanar da Hajji cikin nasara, tare da roƙon su da su yi addu’a ga jihar Zamfara da ma Nijeriya baki ɗaya.

Sanarwar ta fito ne ta hannun mai magana da yawun gwamnan jihar Zamfara, SULAIMAN BALA IDRIS.

Lawal
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • Sulaiman
    ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

MASU ALAKA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Ministan Wajen Sin: Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka Na Da Ma’anar Tarihi

Ministan Wajen Sin: Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka Na Da Ma'anar Tarihi

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.