ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Kafa Tarihi, Yayin Da Aka Fara Jigilar Alhazai Daga Filin Jirgin Sama Na Gusau

by Sulaiman
1 month ago
Lawal

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya kafa sabon tarihi bayan da aka gudanar da jigilar farko na aikin Hajji daga Filin Jirgin Sama na Ƙasa da Ƙasa da ke Gusau.

Jirgin Hajjin na farko ya tashi ne daga filin jirgin ranar Juma’a ɗauke da maniyyata 415 na jihar Zamfara a jirgin kamfanin Max Air mai lamba NGL270 zuwa ƙasar Saudiyya domin gudanar da aikin Hajjin bana.

Rahotanni sun nuna cewa daga cikin maniyyatan akwai maza 288 da mata 127.Da yake jawabi yayin ƙaddamar da tashin jirgin, Gwamna Lawal ya bayyana farin cikin sa da godiyar sa bisa ganin wannan gagarumin ci gaba da ya ce zai kasance abin tarihi a jihar Zamfara.Gwamnan ya bayyana gina Filin Jirgin Sama na Ƙasa da Ƙasa na Gusau a matsayin ɗaya daga cikin manyan ayyukan tarihi da gwamnatin sa ta sa a gaba, kuma alhamdu lillahi, ta cimma nasara.

ADVERTISEMENT

“Ina farin ciki matuƙa a yau ganin maniyyatan mu suna tashi kai tsaye daga Filin Jirgin Sama na Gusau zuwa ƙasar Saudiyya domin aikin Hajjin bana,” in ji gwamnan.

Ya ƙara da cewa, mutane da dama sun yi shakku kan yiwuwar aikin ya zama gaskiya, amma yanzu an tabbatar da hakan bayan an fara aikin gina filin jirgin tun ranar 18 ga watan Yunin 2024.

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

“Ba zan iya bayyana irin farin cikin da nake ciki ba. Wannan babbar dama ce ga maniyyatanmu domin tafiya cikin sauƙi da kwanciyar hankali. Cikin ƙasa da awa huɗu za su isa Saudiyya. A baya kuwa sai sun je Kano ko Sakkwato kafin su samu jirgin Hajji,” in ji gwamnan.

Gwamnan ya ce, wannan nasara wata babban mataki ne na tarihi tare da cika ɗaya daga cikin alƙawuran da ya ɗauka a lokacin yaƙin neman zaɓe.“Wannan tarihi ne mai girma kuma cikar alƙawarin da muka yi wa al’umma. Ina da ƙudurin ci gaba da aiwatar da ayyukan ci gaba domin jihar mu,” in ji shi.

Ya gode wa al’ummar jihar bisa addu’o’insu da kuma amincewar da suka nuna ga gwamnatinsa, yana mai cewa wannan shi ne farkon wasu manyan nasarori.Haka kuma gwamnan ya bayyana cewa gwamnatin jihar ta fara tattaunawa da kamfanonin jiragen sama domin fara zirga-zirgar kasuwanci daga Filin Jirgin Sama na Gusau nan gaba.

A ƙarshe, ya yi wa maniyyatan fatan sauka lafiya da gudanar da Hajji cikin nasara, tare da roƙon su da su yi addu’a ga jihar Zamfara da ma Nijeriya baki ɗaya.

Sanarwar ta fito ne ta hannun mai magana da yawun gwamnan jihar Zamfara, SULAIMAN BALA IDRIS.

Lawal
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • Sulaiman
    Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
  • Sulaiman
    Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

MASU ALAKA

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi
Labarai

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
Labarai

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Next Post
Ministan Wajen Sin: Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka Na Da Ma’anar Tarihi

Ministan Wajen Sin: Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka Na Da Ma'anar Tarihi

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.