ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Wajen Sin: Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka Na Da Ma’anar Tarihi

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 month ago
The U.S. and Chinese flag at the Great Hall of the People prior to the state dinner of President Donald Trump and Chinese President Xi Jinping on Thursday May 14, 2026, in Beijing. (AP Photo/Mark Schiefelbein)

The U.S. and Chinese flag at the Great Hall of the People prior to the state dinner of President Donald Trump and Chinese President Xi Jinping on Thursday May 14, 2026, in Beijing. (AP Photo/Mark Schiefelbein)

Bisa gayyatar da shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya yi masa, shugaban kasar Amurka Donald Trump ya gudanar da ziyara a kasar Sin tsakanin ranar Laraba da Juma’ar makon da muke ciki.

Daga baya a jiya Juma’a, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya yi wa manema labaru karin haske dangane da ganawar da shugabannin kasashen biyu suka yi a wannan karo.

A cewar jami’in na Sin, shugabannin kasashen Sin da Amurka sun yi musayar ra’ayi kan batun raya huldar dake tsakanin kasashensu, da al’amuran da ke faruwa a kasashe da shiyyoyi daban daban, wadanda ke jan hankalin al’ummun duniya, inda tattaunawar da suka yi ta nuna cewa, dukkan kasashen biyu za su iya cimma burinsu na raya kasa, ta hanyar baiwa junansu goyon baya, tare da haifar da alfanu ga al’ummun kasashe daban daban.

ADVERTISEMENT

Ban da haka, Wang Yi ya yi tsokaci kan matsaya daya da shugabannin kasashen Sin da Amurka suka cimma, game da kafa “dangantaka mai dorewa, da amfani bisa manyan tsare-tsare” tsakanin kasashensu.

Ya ce, wannan nau’in dangantaka ya shafi dora muhimmanci kan hadin gwiwar bangarorin 2, da yin takara a tsakaninsu bisa wani tsari mai dacewa, da kokarin cika alkawari, da neman tabbatar da zaman lafiya.Duk a wajen ganawar ta wannan karo, Wang Yi ya ce shugabannin kasashen biyu sun yarda da ci gaba da kokarin yin musayar ra’ayi tsakaninsu.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

Kana bisa gayyatar da shugaba Trump ya yi masa, shugaban kasar Sin Xi Jinping zai kai ziyara kasar Amurka a lokacin kaka na bana. Ban da haka, kasashen 2 za su kara kokarin mu’ammala da juna, don neman daidaita huldar dake tsakaninsu ta fuskar tattalin arziki da cinikayya, da karfafa cudanya a fannonin da suka shafi ilimi, da aikin yada labarai, da masana’antu, da kasuwanci, da dai makamantansu.Haka zalika, babban jami’in na kasar Sin ya ambaci wani batu mai muhimmanci da shugabannin biyu suka tattauna a kai, wato batun yankin Taiwan.

A cewar Wang Yi, matsayin kasar Sin dangane da lamarin a zahiri yake, wato na farko, batun yankin Taiwan batu ne na cikin gida na kasar Sin. Kana na biyu, batun Taiwan yana da matukar muhimmanci ga huldar dake tsakanin Sin da Amurka.

Sa’an nan, na uku, niyyar tabbatar da kwanciyar hankali a mashigin teku na Taiwan ta dace da burin kasashen Sin da Amurka na kare moriyar kansu.

Duk a wajen ganawar a cewar Wang Yi, shugabannin Sin da Amurka sun yi musayar ra’ayoyi dangane da batutuwan yankin Gabas ta Tsakiya da Ukraine, inda shugaba Xi Jinping ya jaddada bukatar komawa teburin shawarwari maimakon ci gaba da amfani da karfin tuwo, ta yadda za a samu damar gaggauta kawo karshen yake-yake. (Bello Wang)

Amurka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Amurka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
‘Ɗan Shekara 30’ Buba Ya Janye Daga Takarar Majalisar Wakilai

'Ɗan Shekara 30' Buba Ya Janye Daga Takarar Majalisar Wakilai

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.