Bisa gayyatar da shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya yi masa, shugaban kasar Amurka Donald Trump ya gudanar da ziyara a kasar Sin tsakanin ranar Laraba da Juma’ar makon da muke ciki.
Daga baya a jiya Juma’a, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya yi wa manema labaru karin haske dangane da ganawar da shugabannin kasashen biyu suka yi a wannan karo.
A cewar jami’in na Sin, shugabannin kasashen Sin da Amurka sun yi musayar ra’ayi kan batun raya huldar dake tsakanin kasashensu, da al’amuran da ke faruwa a kasashe da shiyyoyi daban daban, wadanda ke jan hankalin al’ummun duniya, inda tattaunawar da suka yi ta nuna cewa, dukkan kasashen biyu za su iya cimma burinsu na raya kasa, ta hanyar baiwa junansu goyon baya, tare da haifar da alfanu ga al’ummun kasashe daban daban.
Ban da haka, Wang Yi ya yi tsokaci kan matsaya daya da shugabannin kasashen Sin da Amurka suka cimma, game da kafa “dangantaka mai dorewa, da amfani bisa manyan tsare-tsare” tsakanin kasashensu.
Ya ce, wannan nau’in dangantaka ya shafi dora muhimmanci kan hadin gwiwar bangarorin 2, da yin takara a tsakaninsu bisa wani tsari mai dacewa, da kokarin cika alkawari, da neman tabbatar da zaman lafiya.Duk a wajen ganawar ta wannan karo, Wang Yi ya ce shugabannin kasashen biyu sun yarda da ci gaba da kokarin yin musayar ra’ayi tsakaninsu.
Kana bisa gayyatar da shugaba Trump ya yi masa, shugaban kasar Sin Xi Jinping zai kai ziyara kasar Amurka a lokacin kaka na bana. Ban da haka, kasashen 2 za su kara kokarin mu’ammala da juna, don neman daidaita huldar dake tsakaninsu ta fuskar tattalin arziki da cinikayya, da karfafa cudanya a fannonin da suka shafi ilimi, da aikin yada labarai, da masana’antu, da kasuwanci, da dai makamantansu.Haka zalika, babban jami’in na kasar Sin ya ambaci wani batu mai muhimmanci da shugabannin biyu suka tattauna a kai, wato batun yankin Taiwan.
A cewar Wang Yi, matsayin kasar Sin dangane da lamarin a zahiri yake, wato na farko, batun yankin Taiwan batu ne na cikin gida na kasar Sin. Kana na biyu, batun Taiwan yana da matukar muhimmanci ga huldar dake tsakanin Sin da Amurka.
Sa’an nan, na uku, niyyar tabbatar da kwanciyar hankali a mashigin teku na Taiwan ta dace da burin kasashen Sin da Amurka na kare moriyar kansu.
Duk a wajen ganawar a cewar Wang Yi, shugabannin Sin da Amurka sun yi musayar ra’ayoyi dangane da batutuwan yankin Gabas ta Tsakiya da Ukraine, inda shugaba Xi Jinping ya jaddada bukatar komawa teburin shawarwari maimakon ci gaba da amfani da karfin tuwo, ta yadda za a samu damar gaggauta kawo karshen yake-yake. (Bello Wang)















Discussion about this post