Gwamnan jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayyana shirin kafa kwamitin da zai sake duba tsarin albashin malaman makarantun firamare a fadin jihar, tare da tabbatar wa malamai cewa, gwamnatinsa a tsaye take wajen inganta walwalarsu da tabbatar da cikakken aiwatar da mafi karancin albashi.
Gwamnan ya bayyana hakan ne ranar Talata yayin wata ganawa da malaman firamare, sakatarorin ilimi, shugabannin kananan hukumomi da sauran masu ruwa da tsaki da aka gudanar a dakin taro na shugaban kasa da ke Birnin Kebbi.
Idris ya ce za a bai wa kwamitin kwanaki 30 domin gabatar da rahotonsa da shawarwarinsa kan matsalolin da suka shafi albashi da walwalar malamai.
Ya ce, “Zan kafa kwamitin da zai duba tsarin albashin malaman firamare a fadin jihar. Za a bai wa kwamitin kwanaki 30 domin gabatar da rahotonsa, kuma za mu yi nazari sosai kan shawarwarin da zai bayar.”















Discussion about this post