Kwamitin sulhu na MDD ya gudanar da taron gaggawa kan halin da ake ciki tsakanin Lebanon da Isra’ila a yammacin jiya Litinin.
A jawabinsa yayin taron, wakilin Sin na dindindin a MDD Fu Cong ya nuna cewa, halin da ake ciki tsakanin Lebanon da Isra’ila yana kara ta’azzara, inda Isra’ila ke fadada ayyukanta na soji a Lebanon, tare da ci gaba da habaka abin da ta kira “yankin tsaro”, har ma ta tsallaka kogin Litani, ta mamaye gidan Beaufort. Wannan shi ne aikin soja mafi zurfi da sojojin Isra’ila suka yi a Lebanon cikin shekaru 20 da suka gabata.
Har ila yau, bangaren Isra’ila ya bayyana aniyyarsa ta kara fadada ayyukan sojin kasa, lamarin da al’ummar kasa da kasa suka bayyana damuwa kansa da kuma mummunan sakamakon da zai haifar.
Ya ce, tsagaita wuta tsakanin Lebanon da Isra’ila suna kawai ta tara, kuma dole ne al’ummar kasa da kasa su dauki matakin gaggawa na hana lamarin kara fadawa cikin hali mafi tsanani.
Fu Cong ya yi kira da a cimma tsagaita wuta da dakatar da yaki nan take, don kwantar da tarzoma, da kara tallafa wa Lebanon, don daidaita yanayi cikin gidanta, kuma a tabbatar da cewa rundunar wucin gadi ta MDD a Lebanon (UNIFIL) ta cika aikinta na kiyaye kwanciyar hankali a yankin. (Amina Xu)















Discussion about this post