ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Yaba Da Gudumawar Ɗan Majalisa Hon. Mai Palace A Bangaren Kiwon Lafiya

by Sulaiman
4 months ago
Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jinjina wa ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar mazabar Gusau/Tsafe, Hon. Kabiru Ahmadu Mai Palace, bisa rawar da ya taka wajen inganta harkokin kiwon lafiya a jihar.

 

Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis yayin ƙaddamarwa, sabuntawa tare da faɗaɗa Cibiyar Kiwon Lafiya a Matakin Farko ta Dakta Karima da ke Tudun Wada a Gusau, babban birnin jihar.

ADVERTISEMENT

 

A cewar wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, aikin na daga cikin ayyukan mazaba na shekarar 2025 da Hon. Mai Palace ya aiwatar.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

 

Sanarwar ta nuna cewa, an faɗaɗa cibiyar kiwon lafiyar daga gadon marasa lafiya guda 10 zuwa gadaje 40, tare da samar da ƙarin kayan aiki na zamani domin inganta ayyukan jinya da kula da lafiyar al’umma.

 

Da yake jawabi a wajen ƙaddamarwar, Gwamna Lawal ya bayyana gamsuwarsa da ci gaban da ake samu a bangaren lafiya, yana mai cewa ƙoƙarin san majalisar ya dace da manufofin gwamnatinsa na Shirin Ajanda Shida.

 

Ya ce, ƙoƙarin da ake yi a bangaren lafiya a jihar ya haɗa da samar da magunguna masu muhimmanci, ƙarfafa matakan rigakafi, sabunta manufofin lafiya, tsaftar muhalli, kula da masu juna biyu da yara, da kuma bunƙasa hanyoyin samar da kuɗaɗen tafiya da bangaren lafiya.

 

Gwamnan ya jaddada cewa cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko na taka muhimmiyar rawa wajen kawo sauƙi ga al’umma, domin su ne matakin farko da jama’a ke samun kulawar lafiya kafin a tura su manyan asibitoci.

 

Haka kuma, ya yaba da sauran ayyukan da Hon. Mai Palace ke aiwatarwa a fannin lafiya da ilimi, ciki har da gina cikakken ɗakin kwantar da marasa lafiya a wata cibiyar lafiya da ke Gusau da kuma gyaran gine-gine a babban asibitin Magami.

 

Ya kuma ambaci ayyukan gina ajujuwa da cibiyar jarrabawar kwamfuta (CBT) da ɗan majalisar ke yi a wasu makarantu.

 

A nasa jawabin, Hon. Kabiru Ahmadu Mai Palace ya gode wa gwamnan bisa halartar ƙaddamarwar, yana mai cewa irin waɗannan cibiyoyi na taka muhimmiyar rawa wajen samar da kulawar gaggawa ga al’umma, lamarin da ya sa ya mayar da hankali kan bangaren lafiya a ayyukan mazabarsa.

 

Ƙaddamar da cibiyar, a cewar gwamnatin jihar, na nuna haɗin gwiwa tsakanin bangaren zartarwa da na majalisa wajen kawo ci gaba kai tsaye ga rayuwar jama’a a matakin ƙasa.

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Gwamnatin Sojin Burkina Faso Ta Rushe Duk Jam’iyyun Siyasar Ƙasar

Gwamnatin Sojin Burkina Faso Ta Rushe Duk Jam’iyyun Siyasar Ƙasar

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.