ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Yaba Da Gudumawar Ɗan Majalisa Hon. Mai Palace A Bangaren Kiwon Lafiya

by Sulaiman
7 months ago
Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jinjina wa ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar mazabar Gusau/Tsafe, Hon. Kabiru Ahmadu Mai Palace, bisa rawar da ya taka wajen inganta harkokin kiwon lafiya a jihar.

 

Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis yayin ƙaddamarwa, sabuntawa tare da faɗaɗa Cibiyar Kiwon Lafiya a Matakin Farko ta Dakta Karima da ke Tudun Wada a Gusau, babban birnin jihar.

ADVERTISEMENT

 

A cewar wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, aikin na daga cikin ayyukan mazaba na shekarar 2025 da Hon. Mai Palace ya aiwatar.

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

 

Sanarwar ta nuna cewa, an faɗaɗa cibiyar kiwon lafiyar daga gadon marasa lafiya guda 10 zuwa gadaje 40, tare da samar da ƙarin kayan aiki na zamani domin inganta ayyukan jinya da kula da lafiyar al’umma.

 

Da yake jawabi a wajen ƙaddamarwar, Gwamna Lawal ya bayyana gamsuwarsa da ci gaban da ake samu a bangaren lafiya, yana mai cewa ƙoƙarin san majalisar ya dace da manufofin gwamnatinsa na Shirin Ajanda Shida.

 

Ya ce, ƙoƙarin da ake yi a bangaren lafiya a jihar ya haɗa da samar da magunguna masu muhimmanci, ƙarfafa matakan rigakafi, sabunta manufofin lafiya, tsaftar muhalli, kula da masu juna biyu da yara, da kuma bunƙasa hanyoyin samar da kuɗaɗen tafiya da bangaren lafiya.

 

Gwamnan ya jaddada cewa cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko na taka muhimmiyar rawa wajen kawo sauƙi ga al’umma, domin su ne matakin farko da jama’a ke samun kulawar lafiya kafin a tura su manyan asibitoci.

 

Haka kuma, ya yaba da sauran ayyukan da Hon. Mai Palace ke aiwatarwa a fannin lafiya da ilimi, ciki har da gina cikakken ɗakin kwantar da marasa lafiya a wata cibiyar lafiya da ke Gusau da kuma gyaran gine-gine a babban asibitin Magami.

 

Ya kuma ambaci ayyukan gina ajujuwa da cibiyar jarrabawar kwamfuta (CBT) da ɗan majalisar ke yi a wasu makarantu.

 

A nasa jawabin, Hon. Kabiru Ahmadu Mai Palace ya gode wa gwamnan bisa halartar ƙaddamarwar, yana mai cewa irin waɗannan cibiyoyi na taka muhimmiyar rawa wajen samar da kulawar gaggawa ga al’umma, lamarin da ya sa ya mayar da hankali kan bangaren lafiya a ayyukan mazabarsa.

 

Ƙaddamar da cibiyar, a cewar gwamnatin jihar, na nuna haɗin gwiwa tsakanin bangaren zartarwa da na majalisa wajen kawo ci gaba kai tsaye ga rayuwar jama’a a matakin ƙasa.

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
Gwamnatin Sojin Burkina Faso Ta Rushe Duk Jam’iyyun Siyasar Ƙasar

Gwamnatin Sojin Burkina Faso Ta Rushe Duk Jam’iyyun Siyasar Ƙasar

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.