ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Yaba Da Gudumawar Ɗan Majalisa Hon. Mai Palace A Bangaren Kiwon Lafiya

by Sulaiman
5 months ago
Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jinjina wa ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar mazabar Gusau/Tsafe, Hon. Kabiru Ahmadu Mai Palace, bisa rawar da ya taka wajen inganta harkokin kiwon lafiya a jihar.

 

Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis yayin ƙaddamarwa, sabuntawa tare da faɗaɗa Cibiyar Kiwon Lafiya a Matakin Farko ta Dakta Karima da ke Tudun Wada a Gusau, babban birnin jihar.

ADVERTISEMENT

 

A cewar wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, aikin na daga cikin ayyukan mazaba na shekarar 2025 da Hon. Mai Palace ya aiwatar.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

 

Sanarwar ta nuna cewa, an faɗaɗa cibiyar kiwon lafiyar daga gadon marasa lafiya guda 10 zuwa gadaje 40, tare da samar da ƙarin kayan aiki na zamani domin inganta ayyukan jinya da kula da lafiyar al’umma.

 

Da yake jawabi a wajen ƙaddamarwar, Gwamna Lawal ya bayyana gamsuwarsa da ci gaban da ake samu a bangaren lafiya, yana mai cewa ƙoƙarin san majalisar ya dace da manufofin gwamnatinsa na Shirin Ajanda Shida.

 

Ya ce, ƙoƙarin da ake yi a bangaren lafiya a jihar ya haɗa da samar da magunguna masu muhimmanci, ƙarfafa matakan rigakafi, sabunta manufofin lafiya, tsaftar muhalli, kula da masu juna biyu da yara, da kuma bunƙasa hanyoyin samar da kuɗaɗen tafiya da bangaren lafiya.

 

Gwamnan ya jaddada cewa cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko na taka muhimmiyar rawa wajen kawo sauƙi ga al’umma, domin su ne matakin farko da jama’a ke samun kulawar lafiya kafin a tura su manyan asibitoci.

 

Haka kuma, ya yaba da sauran ayyukan da Hon. Mai Palace ke aiwatarwa a fannin lafiya da ilimi, ciki har da gina cikakken ɗakin kwantar da marasa lafiya a wata cibiyar lafiya da ke Gusau da kuma gyaran gine-gine a babban asibitin Magami.

 

Ya kuma ambaci ayyukan gina ajujuwa da cibiyar jarrabawar kwamfuta (CBT) da ɗan majalisar ke yi a wasu makarantu.

 

A nasa jawabin, Hon. Kabiru Ahmadu Mai Palace ya gode wa gwamnan bisa halartar ƙaddamarwar, yana mai cewa irin waɗannan cibiyoyi na taka muhimmiyar rawa wajen samar da kulawar gaggawa ga al’umma, lamarin da ya sa ya mayar da hankali kan bangaren lafiya a ayyukan mazabarsa.

 

Ƙaddamar da cibiyar, a cewar gwamnatin jihar, na nuna haɗin gwiwa tsakanin bangaren zartarwa da na majalisa wajen kawo ci gaba kai tsaye ga rayuwar jama’a a matakin ƙasa.

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Next Post
Gwamnatin Sojin Burkina Faso Ta Rushe Duk Jam’iyyun Siyasar Ƙasar

Gwamnatin Sojin Burkina Faso Ta Rushe Duk Jam’iyyun Siyasar Ƙasar

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.