ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Zai Halarci Taron Horaswa Na Dabarun Shugabanci A Jami’ar Coventry Ta Ƙasar Birtaniya

by Sulaiman
5 months ago
Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, zai halarci wani babban taron horaswa kan dabarun shugabanci da ƙarfafa tsarin mulki, a wani ɓangare na ƙoƙarin gwamnatinsa na inganta tafiyar da harkokin mulki a jihar.

 

Za a gudanar da taron ne a ranakun 30 da 31 ga watan Maris, 2026, a Jami’ar Coventry da ke Ƙasar Birtaniya, ƙarƙashin jagorancin Cibiyar Nazarin Kasuwanci da Al’umma Masu Ƙarfi, wato Centre for Resilient Business and Society.

ADVERTISEMENT
  • Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Bayar Da Lamba Ga Sabbin Daliban Firamare
  • Matsalar ADC Ta ADC Ce BA Ta APC Ba Ce

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ya bayyana cewa taron yana samun goyon baya daga tsarin tallafin cibiyoyi na Hukumar Bincike da Ƙirƙire-Ƙirƙire ta Ƙasar Birtaniya (UKRI).

 

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Sanarwar ta ƙara da cewa, wannan taro na nuna haɗin gwiwar da ke ƙara ƙarfafawa wajen samar da mafita ta hanyar bincike domin inganta shugabanci, juriyar tsari da ci gaban al’umma a cibiyoyin jihar Zamfara.

 

A cewar sanarwar, ana sa ran gwamnan zai tashi zuwa Birtaniya a ranar Lahadi domin halartar wannan taro na kwanaki biyu, wanda zai haɗa manyan masana daga sassa daban-daban na duniya, masu tsara manufofi da kuma ƙwararru a fannin shugabanci domin tattauna hanyoyin gina tsayayyun cibiyoyi da magance matsalolin al’umma ta hanyar amfani da bincike da bayanai.

 

Muhimman batutuwan da za a tattauna sun haɗa da jagoranci mai juriya a yanayi mai cike da ƙalubale da ƙarancin albarkatu, ƙarfafa tsarin kuɗi, ƙirƙire-ƙirƙire a ɓangaren gwamnati, sarrafa sauye-sauye, da kuma amfani da bayanai cikin gaskiya da ɗa’a wajen tafiyar da mulki.

 

Gwamnan zai halarci taron tare da manyan jami’an gwamnati da suka haɗa da Sakataren Gwamnatin Jihar, kwamishinoni, masu ba da shawara na musamman, da kuma Babban Sakataren Hukumar Bunƙasa Fasahar Sadarwa ta Jihar Zamfara (ZITDA).

 

A wani ɓangare na taron, gwamnan da tawagarsa za su yi wata mu’amala kai tsaye da ɗaliban digiri na biyu da ke gudanar da bincike (PGR), inda za a tattauna kan rawar bincike wajen tsara manufofin gwamnati, tare da jaddada yadda shirin “Ceto Jihar Zamfara” mai ginshiƙai shida ke bayar da darussa a aikace.

 

Wannan zama zai ba da dama ga tattaunawa mai zurfi kan yadda bincike zai wuce ƙa’idar rubuce-rubuce ya zama kayan aiki na zahiri wajen yanke shawara da samar da sakamako mai amfani ga al’umma.

 

Halartar Zamfara a wannan taro na nuna ƙudurin gwamnati wajen haɗa bincike da amfani da bayanai a cikin tafiyar da mulki, domin tallafa wa manufofin shirin “Ceto Jihar Zamfara” wanda ya mayar da hankali kan tsaro, zaman lafiya, noma, lafiya, ilimi, ababen more rayuwa da kuma bunƙasa tattalin arziki.

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
Gyaran Gashi Ya Yi Kyau Da Laushi

Hanyoyin Magance Warin Gashin Kai Ga Mata

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.