ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Zai Halarci Taron Horaswa Na Dabarun Shugabanci A Jami’ar Coventry Ta Ƙasar Birtaniya

by Sulaiman
3 months ago
Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, zai halarci wani babban taron horaswa kan dabarun shugabanci da ƙarfafa tsarin mulki, a wani ɓangare na ƙoƙarin gwamnatinsa na inganta tafiyar da harkokin mulki a jihar.

 

Za a gudanar da taron ne a ranakun 30 da 31 ga watan Maris, 2026, a Jami’ar Coventry da ke Ƙasar Birtaniya, ƙarƙashin jagorancin Cibiyar Nazarin Kasuwanci da Al’umma Masu Ƙarfi, wato Centre for Resilient Business and Society.

ADVERTISEMENT
  • Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Bayar Da Lamba Ga Sabbin Daliban Firamare
  • Matsalar ADC Ta ADC Ce BA Ta APC Ba Ce

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ya bayyana cewa taron yana samun goyon baya daga tsarin tallafin cibiyoyi na Hukumar Bincike da Ƙirƙire-Ƙirƙire ta Ƙasar Birtaniya (UKRI).

 

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

Sanarwar ta ƙara da cewa, wannan taro na nuna haɗin gwiwar da ke ƙara ƙarfafawa wajen samar da mafita ta hanyar bincike domin inganta shugabanci, juriyar tsari da ci gaban al’umma a cibiyoyin jihar Zamfara.

 

A cewar sanarwar, ana sa ran gwamnan zai tashi zuwa Birtaniya a ranar Lahadi domin halartar wannan taro na kwanaki biyu, wanda zai haɗa manyan masana daga sassa daban-daban na duniya, masu tsara manufofi da kuma ƙwararru a fannin shugabanci domin tattauna hanyoyin gina tsayayyun cibiyoyi da magance matsalolin al’umma ta hanyar amfani da bincike da bayanai.

 

Muhimman batutuwan da za a tattauna sun haɗa da jagoranci mai juriya a yanayi mai cike da ƙalubale da ƙarancin albarkatu, ƙarfafa tsarin kuɗi, ƙirƙire-ƙirƙire a ɓangaren gwamnati, sarrafa sauye-sauye, da kuma amfani da bayanai cikin gaskiya da ɗa’a wajen tafiyar da mulki.

 

Gwamnan zai halarci taron tare da manyan jami’an gwamnati da suka haɗa da Sakataren Gwamnatin Jihar, kwamishinoni, masu ba da shawara na musamman, da kuma Babban Sakataren Hukumar Bunƙasa Fasahar Sadarwa ta Jihar Zamfara (ZITDA).

 

A wani ɓangare na taron, gwamnan da tawagarsa za su yi wata mu’amala kai tsaye da ɗaliban digiri na biyu da ke gudanar da bincike (PGR), inda za a tattauna kan rawar bincike wajen tsara manufofin gwamnati, tare da jaddada yadda shirin “Ceto Jihar Zamfara” mai ginshiƙai shida ke bayar da darussa a aikace.

 

Wannan zama zai ba da dama ga tattaunawa mai zurfi kan yadda bincike zai wuce ƙa’idar rubuce-rubuce ya zama kayan aiki na zahiri wajen yanke shawara da samar da sakamako mai amfani ga al’umma.

 

Halartar Zamfara a wannan taro na nuna ƙudurin gwamnati wajen haɗa bincike da amfani da bayanai a cikin tafiyar da mulki, domin tallafa wa manufofin shirin “Ceto Jihar Zamfara” wanda ya mayar da hankali kan tsaro, zaman lafiya, noma, lafiya, ilimi, ababen more rayuwa da kuma bunƙasa tattalin arziki.

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci
  • Sulaiman
    Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026
  • Sulaiman
    Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Gyaran Gashi Ya Yi Kyau Da Laushi

Hanyoyin Magance Warin Gashin Kai Ga Mata

LABARAI MASU NASABA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.