ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Zai Halarci Taron Horaswa Na Dabarun Shugabanci A Jami’ar Coventry Ta Ƙasar Birtaniya

by Sulaiman
4 months ago
Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, zai halarci wani babban taron horaswa kan dabarun shugabanci da ƙarfafa tsarin mulki, a wani ɓangare na ƙoƙarin gwamnatinsa na inganta tafiyar da harkokin mulki a jihar.

 

Za a gudanar da taron ne a ranakun 30 da 31 ga watan Maris, 2026, a Jami’ar Coventry da ke Ƙasar Birtaniya, ƙarƙashin jagorancin Cibiyar Nazarin Kasuwanci da Al’umma Masu Ƙarfi, wato Centre for Resilient Business and Society.

ADVERTISEMENT
  • Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Bayar Da Lamba Ga Sabbin Daliban Firamare
  • Matsalar ADC Ta ADC Ce BA Ta APC Ba Ce

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ya bayyana cewa taron yana samun goyon baya daga tsarin tallafin cibiyoyi na Hukumar Bincike da Ƙirƙire-Ƙirƙire ta Ƙasar Birtaniya (UKRI).

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

Sanarwar ta ƙara da cewa, wannan taro na nuna haɗin gwiwar da ke ƙara ƙarfafawa wajen samar da mafita ta hanyar bincike domin inganta shugabanci, juriyar tsari da ci gaban al’umma a cibiyoyin jihar Zamfara.

 

A cewar sanarwar, ana sa ran gwamnan zai tashi zuwa Birtaniya a ranar Lahadi domin halartar wannan taro na kwanaki biyu, wanda zai haɗa manyan masana daga sassa daban-daban na duniya, masu tsara manufofi da kuma ƙwararru a fannin shugabanci domin tattauna hanyoyin gina tsayayyun cibiyoyi da magance matsalolin al’umma ta hanyar amfani da bincike da bayanai.

 

Muhimman batutuwan da za a tattauna sun haɗa da jagoranci mai juriya a yanayi mai cike da ƙalubale da ƙarancin albarkatu, ƙarfafa tsarin kuɗi, ƙirƙire-ƙirƙire a ɓangaren gwamnati, sarrafa sauye-sauye, da kuma amfani da bayanai cikin gaskiya da ɗa’a wajen tafiyar da mulki.

 

Gwamnan zai halarci taron tare da manyan jami’an gwamnati da suka haɗa da Sakataren Gwamnatin Jihar, kwamishinoni, masu ba da shawara na musamman, da kuma Babban Sakataren Hukumar Bunƙasa Fasahar Sadarwa ta Jihar Zamfara (ZITDA).

 

A wani ɓangare na taron, gwamnan da tawagarsa za su yi wata mu’amala kai tsaye da ɗaliban digiri na biyu da ke gudanar da bincike (PGR), inda za a tattauna kan rawar bincike wajen tsara manufofin gwamnati, tare da jaddada yadda shirin “Ceto Jihar Zamfara” mai ginshiƙai shida ke bayar da darussa a aikace.

 

Wannan zama zai ba da dama ga tattaunawa mai zurfi kan yadda bincike zai wuce ƙa’idar rubuce-rubuce ya zama kayan aiki na zahiri wajen yanke shawara da samar da sakamako mai amfani ga al’umma.

 

Halartar Zamfara a wannan taro na nuna ƙudurin gwamnati wajen haɗa bincike da amfani da bayanai a cikin tafiyar da mulki, domin tallafa wa manufofin shirin “Ceto Jihar Zamfara” wanda ya mayar da hankali kan tsaro, zaman lafiya, noma, lafiya, ilimi, ababen more rayuwa da kuma bunƙasa tattalin arziki.

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
Gyaran Gashi Ya Yi Kyau Da Laushi

Hanyoyin Magance Warin Gashin Kai Ga Mata

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.