Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana matuƙar kaɗuwarsa kan rasuwar tsohon Daraktan Yaɗa Labarai na Hedikwatar Tsaro (DDI), Manjo Janar Rabe Abubakar mai ritaya, wanda ya mutu yayin da yake tsare a hannun ’yan ta’adda a jihar Katsina.
Janar Abubakar, bayan ya shafe shekaru yana hidimtawa ƙasa a aikin soja, ya yi ritaya shekaru kaɗan da suka gabata. An kama shi ne makonni biyu da suka wuce yayin da yake kan hanyarsa ta zuwa garinsu.
A cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Bayo Onanuga, ya fitar, shugaban ƙasar ya jajanta wa iyalan mamacin, musamman matarsa wadda har yanzu take tsare a hannun masu garkuwar.
Haka kuma ya miƙa ta’aziyyarsa ga gwamnatin jihar Katsina da kuma rundunar sojojin Nijeriya.
Shugaban ƙasar ya ce duk da cewa ’yan ta’addan sun aikata abin da suka ga dama, yana so su fahimci cewa gwamnati ba za ta taɓa amincewa da buƙatarsu ta sakin mambobinsu da hukumomin tsaro ke tsare da su ba.
Ya jaddada cewa gwamnatin tarayya za ta ci gaba da yaƙi da ta’addanci da sauran laifukan tsaro ba tare da sassauci ba, tare da tabbatar da cewa ba za ta miƙa wuya ga matsin lambar masu aikata irin waɗannan laifuka ba.















Discussion about this post