Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya ƙaddamar da Kwamitin Haɗin Gwiwa na Hukumomi daban-daban domin yaƙi da matsalar shan miyagun ƙwayoyi, a wani yunƙuri na magance yadda matsalar ke ƙaruwa da kuma illolinta ga al’umma.
Haka kuma, gwamnan ya sanya hannu kan Dokar Zartarwa da ke da nufin daƙile ayyukan ‘yan daba da sauran laifukan da ke da alaƙa da su a faɗin jihar.
An bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Tofa, ya fitar a ranar Laraba.
Gwamna Yusuf ya bayyana cewa shan miyagun ƙwayoyi na daga cikin manyan barazanar da ke fuskantar matasan Kano, yana mai gargadin cewa matsalar na haddasa aikata munanan laifuka, rusa zaman lafiyar iyalai, raunana tattalin arziki da kuma kawo cikas ga zaman lafiya da kwanciyar hankalin al’umma.
Ya ce sabon kwamitin da aka ƙaddamar zai jagoranci daidaita matakan gwamnatin jihar na yaƙi da shan miyagun ƙwayoyi ta hanyar tattara bayanan sirri, tabbatar da bin doka, wayar da kan jama’a, gyaran hali da bayar da shawarwari ga masu ta’ammali da miyagun ƙwayoyi, tare da haɗin gwiwa da hukumomin tsaro da sauran masu ruwa da tsaki.














