Gwamnatin Jihar Kano ta ayyana Talata, 1 ga Satumba, 2026, a matsayin ranar hutu a jihar, domin bai ma’aikata damar gudanar da bikin Takutaha, wato bikin tunawa da ranar haihuwar Annabi Muhammad (SAW).
Daraktar Wayar da Kan Jama’a ta Ofishin Shugaban Ma’aikatan Gwamnati, Rukayya Sulaiman, ce ta bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Laraba.
A cewar sanarwar, hutun ya zo ne a ranar 19 ga Rabi’ul Awwal, 1448AH, domin bai wa ma’aikata da sauran mazauna jihar damar halartar bukukuwan tare da murna da tunani kan rayuwa da koyarwar Annabi Muhammad (SAW).
Shugabar Ma’aikatan Gwamnatin Jihar, Bilkisu Shehu Maimota, ta bukaci ma’aikatan gwamnati da su yi amfani da wannan dama wajen yin tunani tare da aiwatar da kyawawan dabi’un da Annabi Muhammad (SAW) ya koyar, ciki har da gaskiya, hakuri, tausayi, adalci, zaman lafiya da taimakon bil’adama.
Maimota ta kuma bukaci ma’aikata da su ci gaba da kasancewa masu kwarewa, jajircewa da kyawawan dabi’u wajen gudanar da ayyukansu, kamar yadda ka’idojin aikin gwamnati a jihar suka tanada.
Ta yi kira ga mazauna jihar da su gudanar da bikin cikin lumana tare da amfani da wannan lokaci wajen karfafa hadin kai, mutunta juna da zaman lafiya a tsakanin al’ummomin jihar.
Shugabar Ma’aikatan Gwamnatin ta yi addu’ar Allah Ya sa a gudanar da bikin Takutaha cikin zaman lafiya da nasara, tare da yi wa al’ummar jihar fatan murnar wannan rana.














