Kamfanin rarraba wutar lantarki na kasa (TCN) ya sanar da cewa tawagarsa ta musamman mai gudanar da gyaran layukan wutar lantarki ba tare da kashe wuta ba a shiyyar Kaduna ta kammala aikin gyaran layin wutar lantarki mai ƙarfin 132kV da ke tsakanin Zaria da Funtua, ba tare da katse isar da wutar lantarki ga masu amfani ba.
Babbar Manajar Hulɗa da Jama’a ta TCN, Ndidi Mbah, ta bayyana cewa an gudanar da aikin ne daga 4 zuwa 7 ga Yuli, 2026. Ta ce ƙungiyar ta maye gurbin wasu gilasan na’urorin da suka lalace a wasu layin, inda aka yi amfani da haɗin roba da gilashi domin dawo da ingancin tsarin kariyar layin wutar lantarki.
A cewarta, turakun da aka gudanar da aikin sun haɗa da T14, T17, T40, T63, T78, T175, T177 da T178, kuma kowacce daga cikinsu tana da aƙalla gilasai guda biyar da suka lalace. Ta ce jami’an TCN sun samu nasarar maye gurbinsu yayin da layin ke ci gaba da ɗauke da wutar lantarki, lamarin da ya kawar da buƙatar katse wuta domin gudanar da aikin gyaran.
Mbah ta bayyana cewa nasarar aikin na nuna ƙudirin TCN na tabbatar da ingantacciyar hanyar isar da wutar lantarki cikin aminci da inganci. Ta ƙara da cewa kamfanin zai ci gaba da amfani da sabbin fasahohin gyaran layukan wuta ba tare da kashe wuta ba, domin kare tsarin isar da lantarki tare da rage duk wata matsala da ka iya shafar masu amfani da wutar lantarki.













