Gwamnatin Jihar Kaduna ta yaba wa Ofishin Mai Bai Wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Harkokin Tsaro (NSA), kan shirin samar da Dakarun Tsaron Daji, wanda shirye-shiryen ƙaddamar da su suka yi nisa.
Gwamna Uba Sani ne, ya bayyana hakan a ranar Laraba lokacin da ya karɓi wata babbar tawaga daga Ofishin Mai Bai Wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Harkokin Tsaro a Fadar Gwamnati da ke Kaduna.
- Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji
- Shaidar EFCC Ya Ce Sirika Bai Sanya Hannu A Takardun Kwangilar Naira Biliyan 2 Ba
- ’Yan Bindiga Sun Kashe Farfesa Har Lahira A Jihar Benuwai
- Sojoji Sun Hallaka Shugaban ’Yan Bindiga, Sun Daƙile Hare-hare A Zamfara
- Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma
Tawagar, wadda Daraktan Harkokin Tsaro na ofishin, Manjo Janar H. I. Mabeokwu, ya jagoranta, ta kai ziyara ne domin duba yadda ake gudanar da horar da dakarun tsaron daji sama da 1,000 da ake shirin tura su zuwa wuraren da ake fama da matsalar tsaro a faɗin Jihar Kaduna.
A cewar Gwamna Sani, wannan shiri ya nuna ƙudirin Gwamnatin Tarayya na inganta tsaro ta hanyar haɗin gwiwa da gwamnatocin jihohi.
Ya kuma tabbatar da cikakken goyon bayan gwamnatin Kaduna ga shirin, tare da yin alƙawarin ci gaba da kula da jin daɗin waɗanda ake horarwa da kuma masu ba su horo.
Tawagar ta nuna gamsuwarta da ci gaban shirin, inda ta bayyana cewa an tsara horon cikin tsari kuma an samar da kayan aikin da ake buƙata domin gudanar da shi.
Mambobin tawagar sun kuma yaba wa Gwamnatin Jihar Kaduna kan tallafin da take bai wa masu horon da masu koyarwa a lokacin gudanar da atisayen.
Masana harkokin tsaro sun bayyana cewa shirin samar da Dakarun Tsaron Daji zai iya taimakawa wajen inganta tsaro, matuƙar an samar musu da isassun kayan aiki da ababen hawa da za su ba su damar zirga-zirgar a cikin dazuka.



















