Gwamnatin Jihar Katsina ta warware tarin bashin giratuti da ya kai Naira Biliyan 12, wanda hakan ya rage wa ma’aikatan kananan hukumomi da suka yi ritaya kalubalen rayuwa a Jihar.
Shugaban Kungiyar Ma’aikatan Kananan Hukumomi ta Kasa (NULGE), Kwamared Nasir Wada Mai adua, ya bayyana hakan a wata hira ta musamman da LEADERSHIP a ofishinsa.
Ya bayyana wannan ci gaban a matsayin babban taimako ga masu fansho da iyalan ma’aikatan da suka rasu a fadin jihar, ya kara da cewa, biyan wannan bashin na daya daga cikin manyan nasarorin da gwamnatin yanzu ta samu a fannin walwalar ma’aikata.
“Katsina a zahiri jiha ce ta ma’aikata inda kusan kashi 90 cikin 100 na mutanenta, suka dogara da albashi, da fansho. Biyan wannan kudaden babban ci gaba ne,” in ji shi.














Discussion about this post