• Leadership Hausa
Monday, March 27, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Katsina Za Ta Samu Kudaden Bunkasa Ilimi

by Leadership Hausa
5 months ago
in Labarai
0
Gwamnatin Katsina Za Ta Samu Kudaden Bunkasa Ilimi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Katsina za ta sake samun kudin bankin duniya a karkashin shirin nan na inganta ilimi mai suna “BESDA”, domin gudanar da ayyukan ilimi.

Shugaban hukumar ba da ilimin bai-daya na Jihar Katsina, Lawal Buhari Daura ya bayyana hakan a lokacin yake bude taron bunkasa kwazon aiki na kwana 3 domin amfani ga jami’an tattara bayanai da kididdiga na ma’aikatar ilimi.

  • Alkawurana Ga ‘Yan Nijeriya Kan Tsaro, Zaman Kashe Wando Da Tattalin Arziki — Kwankwaso
  • Ma’aikatan N-Power Sun Yi Zanga-Zangar Kin Biyansu Hakkokinsu A Bauchi

Bankin duniya ne karkashin shirin BESDA hadin gwiwa da hukumar ba da ilimin bai daya suka shirya ba da horon a Kano.

Ya ce biyo bayan rahotannin da hukumar tantancewa ta mika ma BESDA, yanzu Jihar Katsina ta cancanci kara samun kudin na bankin duniya domin gudanar da ayyukan BESDA a jihar.

Shugaban hukumar ya ce za a maida hankali wajen amfani da kudaden ga ayyukan da za su kusantar da mutane ga makarantu.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Mai Barin Gado Da Zababbe Sun Fara Cacar Baki Kan Albashin Ma’aikata A Taraba

Abdulaziz Yari Ya Bada Tallafin Tirela 240 Na Abincin Azimi A Zamfara

Ya bukaci wadanda suka halarci horon su maida hankali don ganin sun yi amfani da abin da suka koya a wuraren ayyukansu daban-daban.

Tun da farko, Daraktan sashen tsara bincike da kididdiga na hukumar SUBEB, Lawal Kofar Sauri ya bayyana cewa jami’an da ake ba horon guda 73, an zabo su ne daga kananan hukumomin Jihar Katsina 34 hadi da hukumar SUBEB.

Ya yi nuni da cewa shirin BESDA ya samar da kwamfutocin tafi-da-gidanka, hadi da manyan wayoyon hannu ga jami’an da ke aikin tattara bayanai da kididdiga na hukumar ilimin domin tattara bayanai masu sahihanci da za a yi amfani da su.

Tags: KatsinaKudade
ShareTweetSendShare
Previous Post

Firaministan Sin Ya Bukaci A Inganta Alakar Moriyar Juna Da Kasar Jamus

Next Post

Dan Takarar Gwamnan Kano A P.R.P. Salishu Tanko Yakasai Ya Kaddamar Da Kudure-Kudurensa

Related

Gwamna Mai Barin Gado Da Zababbe Sun Fara Cacar Baki Kan Albashin Ma’aikata A Taraba
Labarai

Gwamna Mai Barin Gado Da Zababbe Sun Fara Cacar Baki Kan Albashin Ma’aikata A Taraba

4 hours ago
Abdulaziz Yari Ya Bada Tallafin Tirela 240 Na Abincin Azimi A Zamfara
Labarai

Abdulaziz Yari Ya Bada Tallafin Tirela 240 Na Abincin Azimi A Zamfara

6 hours ago
2023: INEC Ta Sanar Da Ranar Mika Wa Zababbun Gwamnoni Takardar Shaidar Lashe Zabe
Labarai

2023: INEC Ta Sanar Da Ranar Mika Wa Zababbun Gwamnoni Takardar Shaidar Lashe Zabe

8 hours ago
SERAP Ta Nemi INEC Ta Hukunta Gwamnoni Kan Bangar Siyasa
Labarai

SERAP Ta Nemi INEC Ta Hukunta Gwamnoni Kan Bangar Siyasa

9 hours ago
DSS Ta Cafke Tsohon Soja Da Lauya Da Wasu Kan Zargin Ta’addanci
Labarai

DSS Ta Cafke Tsohon Soja Da Lauya Da Wasu Kan Zargin Ta’addanci

10 hours ago
PDP Ta Dakatar Da Tsofaffin Ministoci 2 Da Wasu 5 Kan Yi Wa Jam’iyyar Zagon-Kasa
Labarai

PDP Ta Dakatar Da Shugabanta Na Kasa Kan Zargin Yi Wa Jam’iyyar Adawa Aiki

19 hours ago
Next Post
Dan Takarar Gwamnan Kano A P.R.P. Salishu Tanko Yakasai Ya Kaddamar Da Kudure-Kudurensa

Dan Takarar Gwamnan Kano A P.R.P. Salishu Tanko Yakasai Ya Kaddamar Da Kudure-Kudurensa

LABARAI MASU NASABA

Kafar CGTN Ta Gabatar Da Jerin Bidiyo Don Yin Bayani Game Da Tsarin Demokuradiyyar Kasar Sin

Kafar CGTN Ta Gabatar Da Jerin Bidiyo Don Yin Bayani Game Da Tsarin Demokuradiyyar Kasar Sin

March 27, 2023
Kafa Dangantakar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Honduras Ya Sake Tabbatar Da Manufar Sin Daya Tak A Duniya

Kafa Dangantakar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Honduras Ya Sake Tabbatar Da Manufar Sin Daya Tak A Duniya

March 27, 2023
Gwamna Mai Barin Gado Da Zababbe Sun Fara Cacar Baki Kan Albashin Ma’aikata A Taraba

Gwamna Mai Barin Gado Da Zababbe Sun Fara Cacar Baki Kan Albashin Ma’aikata A Taraba

March 27, 2023
Abdulaziz Yari Ya Bada Tallafin Tirela 240 Na Abincin Azimi A Zamfara

Abdulaziz Yari Ya Bada Tallafin Tirela 240 Na Abincin Azimi A Zamfara

March 27, 2023
2023: INEC Ta Sanar Da Ranar Mika Wa Zababbun Gwamnoni Takardar Shaidar Lashe Zabe

2023: INEC Ta Sanar Da Ranar Mika Wa Zababbun Gwamnoni Takardar Shaidar Lashe Zabe

March 27, 2023
SERAP Ta Nemi INEC Ta Hukunta Gwamnoni Kan Bangar Siyasa

SERAP Ta Nemi INEC Ta Hukunta Gwamnoni Kan Bangar Siyasa

March 27, 2023
DSS Ta Cafke Tsohon Soja Da Lauya Da Wasu Kan Zargin Ta’addanci

DSS Ta Cafke Tsohon Soja Da Lauya Da Wasu Kan Zargin Ta’addanci

March 27, 2023
Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumi Na 3 A Wasu Birane

Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumi Na 5

March 27, 2023
PDP Ta Dakatar Da Tsofaffin Ministoci 2 Da Wasu 5 Kan Yi Wa Jam’iyyar Zagon-Kasa

PDP Ta Dakatar Da Shugabanta Na Kasa Kan Zargin Yi Wa Jam’iyyar Adawa Aiki

March 26, 2023
Amurka Ta Sake Zargin Kasar Sin Kan Asalin Kwayar Cutar COVID-19 Domin Yunkurin Siyasa

Amurka Ta Sake Zargin Kasar Sin Kan Asalin Kwayar Cutar COVID-19 Domin Yunkurin Siyasa

March 26, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.