ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Kusa Ƙaddamar Da Shirin Yarjejeniyar Ɗa’a Ta Ƙasa, inji Minista 

by Sulaiman
1 year ago
Minista

Gwamnatin Tarayya ta fara himmar ƙaddamar da shirin nan na Yarjejeniyar Ɗa’a ta Ƙasa, da nufin bunƙasa ɗabi’u, ɗa’a da kuma farfaɗo da al’adu a Nijeriya.

 

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya bayyana hakan a lokacin wani taron bita wanda Hukumar Wayar da Kai ta Ƙasa (NOA) ta gudanar a Abuja a ranar Laraba.

ADVERTISEMENT
  • Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Bukaci A Dage Da Addu’o’i 
  • Ta’addancin ‘Yan Ta’adda A Kan Sarakuna

A wata sanarwa da Rabiu Ibrahim, Mataimaki na Musamman ga Ministan kan Harkokin Yaɗa Labarai, ya raba wa manema labarai, Idris ya bayyana cewa ma’aikatar sa, ta hanyar NOA, ta tsara wannan gagarumin shirin ne domin dukkan ‘yan Nijeriya su samu cikakkiyar fahimta dangane da haƙƙoƙin su a ƙarƙashin tsarin mulkin ƙasa da kuma dokokin ƙasa, sannan su ma gwamnatoci a kowane mataki su san dukkan haƙƙoƙin al’umma da suka rataya a wuyan su kamar yadda tsarin mulki ya tanada.

 

LABARAI MASU NASABA

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

“A ɓangare ɗaya, domin tabbatar da cewa dukkan ‘yan Nijeriya su san ‘yancin su da kariyar da suke da ita a ƙarƙashin tsarin mulki da dokokin ƙasa sannan kuma gwamnatoci a kowane mataki su san duk wani nauyi na jama’a da kundin tsarin mulki ya ɗora masu. Wannan burin na farko an rubuta shi a cikin ‘Manyan Alƙawurra ‘ bakwai na Yarjejeniyar.

 

“A ɗaya ɓangaren kuma, a wayar da kan dukkan ‘yan Nijeriya kan dukkan nauyin da ya rataya a wuyan mu a matsayin mu na ‘yan wannan ƙasa mai girma da kyau – wanda ke nufin nauyin da ya rataya a wuyan mu ba kawai ga junan mu ba ne, har ma ga gwamnati da ƙasa. Wannan burin na biyu an rubuta shi a cikin ‘Muhimman Alƙawurra’ bakwai na Yarjejeniyar.”

 

Idris ya sha alwashin ci gaba da aiki gadan-gadan babu kama hannun yaro da nufin ganin an samar da ƙasa inda ‘yan ƙasa da ‘ya’yan ta suke ƙaunar juna da girmama juna.

 

Ministan ya ce NOA ta zama ɗaya daga cikin hukumomi masu tasiri wajen sauya tunanin jama’ar ƙasa, kawo haɗin kai a ƙasar mai jama’a daban-daban, tare da kawo jituwa da natsuwa a kowane sashe na ƙasar.

 

Ya ce, “Na yi murna da ganin cewa NOA a ƙarƙashin jagorancin Mista Issa-Onilu, ta ba da muhimmanci ga fasahar zamani a aikin hukumar, tana tafiya tare da halin da ake ciki a ƙarni na 21.

 

“NOA ta zama ɗaya daga cikin hukumomi waɗanda suka fi yin aiki da fasahar zamani a Nijeriya a yau, suna kan gaba wajen amfani da kayan aiki na fasahar zamani kamar su manhajar The Mobiliser da kuma Fasahar Komfuta (AI) da kowa ya karɓa wajen ƙara wayar da kan jama’a.

 

Idris ya bayyana wannan babban taron bitar a matsayin wani muhimmin mataki da ya dace, wanda aka yi hangen nesa domin samar da wata dama wajen inganta tare da ƙara wa hukumar NOA ƙaimi da nufin tsara kyakkyawar makomar Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle
Manyan Labarai

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS
Labarai

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025
ECOWAS
Labarai

A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS

November 16, 2025
Next Post
Yadda Talauci Da Jahilci Ke Kara Yawaitar Safarar Sassan Jikin Dan Adam A Nijeriya

Yadda Talauci Da Jahilci Ke Kara Yawaitar Safarar Sassan Jikin Dan Adam A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025
ECOWAS

A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS

November 16, 2025
APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

November 16, 2025
Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

November 16, 2025
Kwankwaso

NNPP Tana Da Ƙwarin Gwiwar Riƙe Kano Da Lashe Jihohin Arewa A Zaɓen 2027 – Ajuji

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.