ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, June 23, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Zamfara Ta Jaddada Aniyarta Na Ƙin Sulhu Da ‘Yan Ta’adda

by Sulaiman
2 hours ago
Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya sake jaddada matsayar gwamnatin sa na ƙin shiga tattaunawa ko ƙulla yarjejeniyar sulhu da ’yan bindiga, yana mai cewa gwamnatin jihar ba za ta amince da zaman sulhu da ƙungiyoyin masu aikata laifuka ba.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a wata hira da ya yi da Sashen Hausa na BBC, wadda aka saurara a Kaduna, inda ya ce gwamnatinsa na ci gaba da goyon bayan dabarar yaƙi da rashin tsaro ta hanyar amfani da jami’an tsaro maimakon tattaunawa da masu aikata laifuka.

Dauda Lawal ya ce ba abin yarda ba ne ga kowane mutum ko ƙungiya ta shiga tsakani wajen ƙulla yarjejeniyar zaman lafiya da ’yan bindiga, yana mai jaddada cewa duk wanda ke yin hakan yana yi ne a madadinsa ba tare da wakiltar gwamnatin jihar ba.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, tun daga farkon mulkinsa gwamnati ta tsaya tsayin daka kan cewa ba za ta yi sulhu da ƙungiyoyin da ke da alhakin kashe-kashe, garkuwa da mutane da kai hare-hare kan al’ummomi a faɗin jihar ba.“Ra’ayin neman sulhu da ’yan bindiga ba ra’ayina ba ne, kuma ba zai taɓa zama haka ba,” in ji gwamnan, yana mai jaddada cewa gwamnatin jihar ba za ta yi sassauci da masu aikata laifuka ba.

Gwamnan ya bayyana cewa wasu rahotannin da ke yawo kan cewa an samu yarjejeniyar sulhu a wasu sassan jihar ba su samu amincewar gwamnatin Zamfara ba.

LABARAI MASU NASABA

Sowore Ya Sha Alwashin Ci Gaba Da Gwagwarmaya Duk Da Tsare Shi A Gidan Yarin Kuje

Amurka Ta Dakatar Da Takunkumin Man Fetur Kan Iran

Ya ce gwamnatin jihar ba ta da hannu a irin waɗannan shirye-shirye, kuma ba ta sauya matsayarta kan yadda za a magance matsalar tsaro ba.

Lawal ya nuna cikakken kwarin gwiwa kan cewa jami’an tsaro za su iya kawo ƙarshen ayyukan ’yan bindiga, yana mai cewa babu wata ƙungiyar masu laifi da ta fi ƙarfin gwamnatin Najeriya.“Gwamnati ta fi ƙarfin kowace ƙungiyar ’yan bindiga,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa ci gaba da gudanar da hare-haren tsaro tare da haɗin kai tsakanin hukumomin tsaro zai taimaka wajen dawo da zaman lafiya mai ɗorewa a jihar.

Gwamnan ya tunatar da cewa an yi ƙoƙarin yin sulhu da ’yan bindiga a baya, amma hakan bai samar da mafita ba.A maimakon haka, ya ce irin waɗannan yarjejeniyoyi sun ƙara wa masu aikata laifukan ƙarfin guiwa tare da ba su damar ci gaba da ayyukansu.

A cewarsa, dabarar tsaron da ake aiwatarwa yanzu a Zamfara ta fara nuna sakamako mai kyau, inda wasu yankunan da a baya suka yi ƙaurin suna wajen hare-haren ’yan bindiga suka fara samun kwanciyar hankali sakamakon ƙara zafafa ayyukan soji.

Dauda Lawal ya yi kira ga al’ummar jihar da su ci gaba da nuna haƙuri tare da bai wa jami’an tsaro haɗin kai a yaƙin da ake yi da rashin tsaro.

Ya tabbatar musu da cewa gwamnati ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen lalata hanyoyin sadarwa da sansanonin masu aikata laifuka.Gwamnan ya sake nanata cewa hanya mafi dacewa ta samar da zaman lafiya mai ɗorewa a Zamfara ita ce ɗaukar mataki mai tsauri kan ’yan bindiga, ba ta hanyar shiga tattaunawar sulhu da su ba.

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    An Bude Bikin Baje Kolin Hada-Hadar Samar Da Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Karo Na Hudu
  • Sulaiman
    Kudin Shigar Gwamnatin Sin Ya Karu Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    Sowore Ya Sha Alwashin Ci Gaba Da Gwagwarmaya Duk Da Tsare Shi A Gidan Yarin Kuje
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Zai Halarci Taron Dandalin Tattaunawar Davos Na Lokacin Zafi Karo Na 17

MASU ALAKA

Sowore Ya Sha Alwashin Ci Gaba Da Gwagwarmaya Duk Da Tsare Shi A Gidan Yarin Kuje
Labarai

Sowore Ya Sha Alwashin Ci Gaba Da Gwagwarmaya Duk Da Tsare Shi A Gidan Yarin Kuje

June 22, 2026
Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
Kasashen Ketare

Amurka Ta Dakatar Da Takunkumin Man Fetur Kan Iran

June 22, 2026
Ya Kamata Farashin Siminti Ya Sauka — Umahi Ga Masana’antun Siminti
Manyan Labarai

Ya Kamata Farashin Siminti Ya Sauka — Umahi Ga Masana’antun Siminti

June 22, 2026
Next Post
An Bude Bikin Baje Kolin Hada-Hadar Samar Da Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Karo Na Hudu

An Bude Bikin Baje Kolin Hada-Hadar Samar Da Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Karo Na Hudu

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

An Bude Bikin Baje Kolin Hada-Hadar Samar Da Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Karo Na Hudu

An Bude Bikin Baje Kolin Hada-Hadar Samar Da Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Karo Na Hudu

June 22, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Jaddada Aniyarta Na Ƙin Sulhu Da ‘Yan Ta’adda

Gwamnatin Zamfara Ta Jaddada Aniyarta Na Ƙin Sulhu Da ‘Yan Ta’adda

June 22, 2026
Kudin Shigar Gwamnatin Sin Ya Karu Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

Kudin Shigar Gwamnatin Sin Ya Karu Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

June 22, 2026
Sowore Ya Sha Alwashin Ci Gaba Da Gwagwarmaya Duk Da Tsare Shi A Gidan Yarin Kuje

Sowore Ya Sha Alwashin Ci Gaba Da Gwagwarmaya Duk Da Tsare Shi A Gidan Yarin Kuje

June 22, 2026
Firaministan Sin Zai Halarci Taron Dandalin Tattaunawar Davos Na Lokacin Zafi Karo Na 17

Firaministan Sin Zai Halarci Taron Dandalin Tattaunawar Davos Na Lokacin Zafi Karo Na 17

June 22, 2026
Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

June 22, 2026
Sin Ta Jawo Jarin Waje Yuan Biliyan 327.29 Daga Janairu Zuwa Mayu Na Bana

Sin Ta Jawo Jarin Waje Yuan Biliyan 327.29 Daga Janairu Zuwa Mayu Na Bana

June 22, 2026
2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-23 Sun Samu Horaswar Farko Kan Ceto Mara Lafiya A Da’irar Sama

‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-23 Sun Samu Horaswar Farko Kan Ceto Mara Lafiya A Da’irar Sama

June 22, 2026
Sin Ta Kara Sassa 10 Na Kasar Amurka Cikin Jerin Bangarorin Da Ta Haramta Fitar Da Hajoji Zuwa Gare Su

Sin Ta Kara Sassa 10 Na Kasar Amurka Cikin Jerin Bangarorin Da Ta Haramta Fitar Da Hajoji Zuwa Gare Su

June 22, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.