Jam’iyyar PRP ta yi watsi da zargin cewa tsohon gwamnan Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, ya sayi fom ɗin takara 69 a wani yunƙuri na karɓe ikon jam’iyyar gabanin zaɓen 2027.
Jam’iyyar ta bayyana zargin a matsayin ƙarya da kuma kawo ruɗani da shakku ga magoya bayan jam’iyyar.
Martanin PRP ya biyo bayan ikirarin da Abdulkadir Musa Giza ya yi, inda ya bayyana kansa a matsayin shugaban Dandalin Masu Ruwa da Tsaki na Arewa maso Yamma na PRP, yana zargin cewa Kwankwaso ya mamaye tsarin jam’iyyar.
Da yake zantawa da manema labarai a Abuja ranar Litinin, Sakataren Ƙasa na PRP, Musa Maigari, ya musanta zargin tare da jaddada cewa Kwankwaso ba shi da wata alaƙa a hukumance da jam’iyyar.
A cewarsa, an riga an cike dukkan muƙaman jam’iyyar kuma an kammala zaɓukan fidda gwani.
Ya kuma yi tambaya kan sahihancin wanda ya yi zargin, yana mai cewa mutumin ba mamba ba ne na PRP, don haka ba ya da hurumin yin irin waɗannan maganganu a madadin jam’iyyar.
PRP ta sake jaddada cewa tsarin jam’iyyar yana nan daram kuma babu wani mutum daga waje da ya mallaki ko ya karɓe jagorancin ta.














Discussion about this post