Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin Guo Jiakun, ya sanar da cewa firaministan kasar Li Qiang zai halarci taron dandalin tattaunawar Davos na lokacin zafi karo na 17 a birnin Dalian daga ranar 23 zuwa 24 ga Yuni. Ya bayyana cewa taron muhimmin dandali ne na inganta mu’amala da hadin gwiwa mai amfani tsakanin Sin da sauran kasashe. Ban da haka kuma, firaministoci daga Bangladesh, Guinea, Kazakhstan, Koriya ta Kudu, Mongolia, da Montenegro da na sauran kasashe su ma za su halarci taron.
Guo ya bayyana hakan ne a gun taron manema labarai na yau da kullum da aka gudanar yau Litinin. Dangane da ziyarar da ministar wajen Austria Beate Meinl-Reisinger za ta kawo Sin, Guo ya bayyana cewa Sin tana son yin aiki tare da Austria don inganta samun babban ci gaba na abokantaka bisa muhimman tsare-tsare a tsakaninsu. Ya kuma ambaci cewa firaministan Bangladesh Tarique Rahman zai kawo ziyara a Sin daga ranar 24 zuwa 26 ga Yuni.
Bugu da kari, lokacin da aka ambaci batun amfani da dan’adam wajen gwaje-gwaje da kuma yakin kwayoyin cuta da sojojin Japan suka yi a lokacin Yakin Duniya na Biyu, Guo ya ce miyagun ayyukan sojojin Japan za su dade suna kasancewa abin kunya a tarihin dan’adam. Kana ya ce, “Farfado da ra’ayin nuna karfin soji” da Japan ke yi a halin yanzu, mataki ne na koma baya, kuma ba zai yi nasara ba.
Bugu da kari, game da mummunan yanayin barkewar cutar Ebola a halin yanzu, Guo ya ce gwamnatin Sin ta yanke shawarar sake samar da agajin gaggawa ga kasashen jamhuriyar demokradiyyar Kongo da Uganda, da kuma kungiyar Tarayyar Afirka, da sauransu.(Safiyah Ma)















Discussion about this post