Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar AAC, Omoyele Sowore, ya bayyana cewa tsare shi ba zai hana shi ci gaba da fafutukar gwagwarmaya da wayar da kan al’umma ba.
Sowore ya yi wannan bayani ne a ranar Litinin bayan wata kotun tarayya da ke Abuja ta ba da umarnin tsare shi a gidan gyaran hali na Kuje har zuwa lokacin ci gaba da sauraron shari’ar da ake yi masa.
Alƙalin kotun, Justice Mohammed Umar, ne ya bayar da umarnin bayan soke belin da aka ba Sowore a baya.
Hakan ya biyo bayan ƙin amincewar kotun da buƙatar da Sowore ya gabatar na neman alƙalin ya janye daga shari’ar da ake yi masa, wadda ta shafi wasu kalamai da ake zargin ya yi inda ya bayyana Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, a matsayin mai aikata laifi.
Da yake magana bayan yanke hukuncin, Sowore ya ce tsare shi ba zai karya masa guiwa ba.
Sowore ya jaddada cewa zai ci gaba da tsayawa kan manufofinsa da fafutukar da yake yi duk da ƙalubalen da yake fuskanta a kotu.














Discussion about this post