Ministan Ayyuka, David Umahi, ya yi kira ga masana’antun siminti a faɗin ƙasar nan da su gaggauta rage farashin siminti, yana mai cewa tsadarsa ta na kawo cikas ga ayyukan gine-ginen more rayuwa da ake gudanarwa tare da ƙara yawan buƙatar sake duba kuɗaɗen kwangiloli.
Umahi ya bayyana hakan ne yayin da yake gabatar da jawabi a taron ƙaddamar da sabon sunan da aka sauya na kamfanin Lafarge, wanda yanzu ya koma HBM, kuma mamba a rukunin kamfanonin HUAXIN Group, a birnin Legas ranar Lahadi.
Da yake jawabi a gaban shugabannin masana’antu, da masu zuba jari da sauran masu ruwa da tsaki, ministan ya jaddada cewa Gwamnatin Tarayya za ta fara tattaunawa da masana’antun siminti daga ranar 1 ga Yuli domin samo mafita kan matsalar tsadar siminti.
Ya kuma buƙaci kamfanin HBM da sauran kamfanonin da ke harkar siminti da su faɗaɗa ƙarfin samar da kayayyakinsu domin biyan buƙatun da ke ƙaruwa sakamakon manyan ayyukan raya abaɓen more rayuwa da ake aiwatarwa a ƙasar.
Umahi ya yaba wa kamfanin bisa sauyin da ya samu da kuma ci gaba da jajircewarsa wajen zuba jari a kasuwar ƙasar nan, tare da tabbatar wa mahukuntansa cewa gwamnati za ta ci gaba da ba su goyon baya da haɗin gwiwa.
Ministan ya kuma bayyana irin ci gaban da ake samu ƙarƙashin manufofi “Renewed Hope Agenda” na Shugaba Bola Ahmed Tinubu, musamman a fannin gine-gine da bunƙasa abaɓen more rayuwa.















Discussion about this post