Gwamnatin Jihar Zamfara ta fara shirin mayar da yara 453,602 da ba sa zuwa makaranta cikin tsarin karatu a faɗin ƙananan hukumomin jihar 14.
Hukumar Ilimin Bai Ɗaya ta Zamfara (ZSUBEB) ce ta fara shirin tare da tallafin UNICEF da sauran masu ruwa da tsaki, domin tabbatar da cewa yaran da aka gano sun koma makaranta.
Shugaban ZSUBEB, Farfesa Nasiru Garba Anka, ya ce kashi 95.3 cikin 100 na yaran suna zaune ne a yankunan karkara, yayin da kashi 4.7 ke zaune a garuruwan ƙananan hukumomi.
Ya ce yanzu babban abin da ya fi muhimmanci shi ne a mayar da yaran makaranta, a tabbatar sun ci gaba da zuwa, sannan su samu ingantaccen ilimi.
Anka ya bayyana matsalar yaran da ba sa zuwa makaranta a matsayin babbar matsala da ta shafi Nijeriya baki ɗaya.
Ya kuma yi kira ga sarakunan gargajiya, shugabannin addini, shugabannin al’umma da sauran masu ruwa da tsaki da su taimaka wajen ganin yaran sun koma makaranta.
Ya ce shirin zai taimaka wajen bai wa dubban yara a Zamfara damar samun ilimi.













