Rahotanni na cewa, hadin gwiwar Sin da Afrika a bangarori daban-daban ya samu ci gaba sosai a farkon bana, inda darajar cinikayya tsakanin bangarorin biyu ta haura yuan biliyan 800 a karon farko cikin watanni 4 na farkon bana, idan aka kwatanta da makamancin lokacin a baya. Manazarta daga kasashen Afrika da dama sun bayyana dangantakar bangarorin biyu a matsayin mai gaggauta haifar da ci gaba a nahiyar Afrika, inda wasu kafafen yada labarai suka yi kira ga kasar Eswatini ta kulla huldar diplomasiyya da Sin tun da wuri, domin kada ta ci gaba da rasa damarmakin samun ci gaba.
Da yake amsa tambayoyi yayin taron manema labarai na yau Talata, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun ya bayyana cewa, karkashin tsarin dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afrika wato FOCAC a takaice da shawarar Ziri Daya da Hanya Daya, ana samun tagomashi daga dukkan hadin gwiwar da ake yi tsakanin Sin da Afrika, wanda ke bunkasa harkokin masana’antu da zamanantar da aikin gona a kasashen nahiyar, tare da samar da kwararan alfanu ga al’ummar nahiyar.
Ya kara da cewa, tun daga ranar 1 ga watan Mayun bana, kasar Sin ta fara aiwatar da manufar soke haraji baki daya kan kayayyakin kasashen Afrika 53 da ke da huldar diplomasiyya da ita. Kuma yayin da katafariyar kasuwar Sin ta bude kofarta ga nahiyar Afrika, suna fatan dukkan kasashen nahiyar za su shiga hadin gwiwar Sin da Afrika, domin su amfana da ci gaba cikin sauri na Sin da karfafa abotar bangarorin biyu da kuma cimma burin zamanantar da Sin da Afrika. (Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post