Babban Limamin Cocin Katolika na Diocese da ke Sakkwato, Matthew Hassan Kukah, ya bayyana cewa tsohon Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nasir El-Rufai, ya taɓa ƙwace filin tsohon Shugaban Mulkin Soja na Nijeriya, Yakubu Gowon, da ke Abuja.
Kukah ya bayyana hakan ne a ranar Talata yayin bitar littafin tarihin rayuwar Gowon mai suna “My Life of Duty and Allegiance” a Abuja.
A cewarsa, bayan an yi wa Gowon juyin mulki a 1975 kuma ya dawo daga gudun hijira daga Birtaniya, bai mallaki ko da fili ɗaya a Abuja ba.
Ya ce tsohon shugaban mulkin soja, Ibrahim Babangida, tare da wasu manyan hafsoshin soja ne suka taimaka masa wajen samun filin.
Kukah ya ce Gowon ya fara gina gida a filin kafin daga bisani aka ƙwace shi a lokacin da El-Rufai yake ministan Abuja.
Sai dai ya bayyana cewa tsohon Janar, Theophilus Danjuma, da wasu manyan mutane sun shiga tsakani har aka mayar wa Gowon filin nasa.
Limamin ya kuma bayyana irin wahalhalun da Gowon da iyalansa suka sha yayin gudun hijira a Birtaniya.
Ya ce Gowon ya sha fama wajen samun aiki har ma da buɗe asusun banki, yayin da matarsa Victoria Gowon ke tallafa wa iyalin ta hanyar ɗinkin zanin gado da yin matasai tana sayarwa.
Kukah ya ƙara da cewa wani ma’aikacin gida da aka tura domin taimaka wa iyalin daga Nijeriya, daga baya an gano cewa leƙen asiri yake yi a kansu, amma bai samu wani abin kai rahoto ba.
Ya bayyana littafin tarihin Gowon mai kusan shafuka 900 a matsayin muhimmin tarihi da ya ƙunshi bayanai kan juyin mulki, gudun hijira, shugabanci da kuma rayuwar tsohon shugaban ƙasar.















Discussion about this post