ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda El-Rufai Ya Ƙwace Filin Gowon A Abuja — Bishop Kukah

by Sadiq
2 months ago

Babban Limamin Cocin Katolika na Diocese da ke Sakkwato, Matthew Hassan Kukah, ya bayyana cewa tsohon Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nasir El-Rufai, ya taɓa ƙwace filin tsohon Shugaban Mulkin Soja na Nijeriya, Yakubu Gowon, da ke Abuja.

Kukah ya bayyana hakan ne a ranar Talata yayin bitar littafin tarihin rayuwar Gowon mai suna “My Life of Duty and Allegiance” a Abuja.

A cewarsa, bayan an yi wa Gowon juyin mulki a 1975 kuma ya dawo daga gudun hijira daga Birtaniya, bai mallaki ko da fili ɗaya a Abuja ba.

ADVERTISEMENT

Ya ce tsohon shugaban mulkin soja, Ibrahim Babangida, tare da wasu manyan hafsoshin soja ne suka taimaka masa wajen samun filin.

Kukah ya ce Gowon ya fara gina gida a filin kafin daga bisani aka ƙwace shi a lokacin da El-Rufai yake ministan Abuja.

LABARAI MASU NASABA

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Sai dai ya bayyana cewa tsohon Janar, Theophilus Danjuma, da wasu manyan mutane sun shiga tsakani har aka mayar wa Gowon filin nasa.

Limamin ya kuma bayyana irin wahalhalun da Gowon da iyalansa suka sha yayin gudun hijira a Birtaniya.

Ya ce Gowon ya sha fama wajen samun aiki har ma da buɗe asusun banki, yayin da matarsa Victoria Gowon ke tallafa wa iyalin ta hanyar ɗinkin zanin gado da yin matasai tana sayarwa.

Kukah ya ƙara da cewa wani ma’aikacin gida da aka tura domin taimaka wa iyalin daga Nijeriya, daga baya an gano cewa leƙen asiri yake yi a kansu, amma bai samu wani abin kai rahoto ba.

Ya bayyana littafin tarihin Gowon mai kusan shafuka 900 a matsayin muhimmin tarihi da ya ƙunshi bayanai kan juyin mulki, gudun hijira, shugabanci da kuma rayuwar tsohon shugaban ƙasar.

MASU ALAKA

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi
Manyan Labarai

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe
Manyan Labarai

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
Manyan Labarai

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Next Post
Lalong Da Sauran ‘Yan Takarar APC Sun Lashe Zaben Fidda Gwani Na Majalisar Dokoki A Filato

Lalong Da Sauran 'Yan Takarar APC Sun Lashe Zaben Fidda Gwani Na Majalisar Dokoki A Filato

LABARAI MASU NASABA

Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

July 17, 2026
Yawan Mu’amalar Kudi Tsakanin Mazauna Sin Da ’Yan Kasashen Waje Ya Hau Wani Sabon Matsayi A Tarihi

Yawan Mu’amalar Kudi Tsakanin Mazauna Sin Da ’Yan Kasashen Waje Ya Hau Wani Sabon Matsayi A Tarihi

July 17, 2026
Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

July 17, 2026
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Babban Taron AI Na Duniya Na 2026 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Babban Taron AI Na Duniya Na 2026 Tare Da Gabatar Da Jawabi

July 17, 2026
Falalar Salatut Tasbihi

Falalar Salatut Tasbihi

July 17, 2026
A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

July 17, 2026
Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

July 17, 2026
Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

July 17, 2026
Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.