Tun daga ranar 1 zuwa 7 ga wannan wata, shugaban kasar Uruguay Yamandu Orsi ya kawo ziyara kasar Sin, batun ya jawo hankalin kafofin watsa labaru na kasa da kasa. Shugaba Orsi, shi ne shugaba na farko na kasar nahiyar Latin Amurka da ya kawo ziyara Sin a wannan sabuwar shekara, kana kasar Uruguay ta kasance mai jagorancin kungiyar G77 da Sin, da kungiyar hadin gwiwar kasashen Latin Amurka da Caribbean, da kuma kungiyar kasuwar kasashe masu tasowa wato MERCOSUR. Wannan ya shaida cewa, ziyarar shugaba Orsi a kasar Sin ba ta shafi bangarorin biyu kawai ba ne, har ma ta shaida sha’awar kasashen Latin Amurka da kasashe masu tasowa na duniya ga kasar Sin domin yin hadin gwiwa da samun bunkasa tare.
Kasar Uruguay tana yankin nahiyar kudancin Amurka ce, sada zumunta a tsakanin Sin da Uruguay ya kasance misali yayin da ake raya dangantakar dake tsakanin Sin da kasashen Latin Amurka, har ma da kasashe masu tasowa baki daya. A halin yanzu, ana fuskantar sauyin yanayi da yin kwaskwarima a duniya, tare da ra’ayoyin bangare daya da ba da kariya ga cinikayya. Ana bukatar kasashe masu tasowa su kara yin hadin gwiwa da samun bunkasa tare don tabbatar da ci gaban duk duniya baki daya.
A yayin ziyarar shugaba Orsi a kasar Sin, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi shawarwari tare da shi, inda shugaba Xi ya jaddada cewa, Sin tana son yi kokari tare da kasar Uruguay wajen kara yin hadin gwiwa a tsakanin kasashe masu tasowa, da sa kaimi ga raya bangarori daban daban a duniya cikin adalci, da raya tattalin arziki bisa tsarin bai-daya a duniya baki daya.
Shugaba Orsi yana son yin hadin gwiwa tare da kasar Sin wajen tabbatar da moriyar kasashe masu tasowa na duniya tare. Wannan ya shaida cewa, kasashen biyu sun maida hankali ga hadin gwiwa, da sa kaimi ga samun adalci a duniya baki daya. (Zainab Zhang)















Discussion about this post