Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON) ta sanar da samun nasarar kammala jigilar maniyyata aikin Hajjin 2026 zuwa kasar Saudiyya.
A cikin wata sanarwa da hukumar ta fitar ranar Alhamis, ta ce jirgin karshe na jigilar maniyyata ya tashi da misalin karfe 10:44 na safe a ranar 21 ga Mayu, inda jirgin Max Air ya dauki maniyyata daga jihar Zamfara ta filin jirgin sama na Gusau.
Aikin jigilar, wanda ya fara ranar 3 ga Mayu, ya kunshi jimillar jirage 98 cikin kwanaki 18 — daidai da kusan jirage biyar a kullum.
Kasar Saudiyya, ta ware wa Nijeriya guraben maniyyata 50,000 domin aikin Hajjin 2026, ciki har da gurabe 9,750 da aka tanada domin kamfanonin yawon bude ido masu lasisi, jami’ai da ma’aikatan tallafi.















Discussion about this post