ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hanyar Mota Daga Gabashi Zuwa Yammacin Aljeriya Kyakkyawan Misali Ne Ga Hadin-Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Raya Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya”

by CMG Hausa
3 years ago
Aljeriya

Kwanan nan ne aka kaddamar da wata babbar hanyar mota, wadda ta tashi daga gabashi zuwa yammacin kasar Aljeriya, wadda kamfanin kasar Sin ya shimfida. Hanya ce da ta samu babban yabo daga al’ummar wurin, kana kyakkyawan abun misali ce ga hadin-gwiwar Sin da Aljeriya, har ma da Sin da Afirka, a fannin raya shawarar “ziri daya da hanya daya”. 

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Wang Wenbin, ya bayyana a yau Litinin cewa, kasarsa na fatan yin kokari tare da kasar Aljeriya, da ma sauran kasashe, wajen kara bunkasa shawarar “ziri daya da hanya daya”, ta yadda za’a taimaka ga farfado da tattalin arziki, gami da ci gaban duniya mai dorewa.

  • Kamfanin Gine-gine Na CITIC Ya Mika Sashen Karshe Na Aikin Ginin Babbar Hanyar Mota A Aljeriya

A shekaranjiya Asabar ne kamfanin gine-gine na kasar Sin CITIC ya mika sashen karshe na aikin ginin babbar hanyar mota da ta hade sassan larduna 17 dake kasar Aljeriya. Karkashin babban aikin ginin hanyar, CITIC ya kammala ginin kilomita 84 na hanyar.

ADVERTISEMENT

Hanyar wadda ta hade sassan gabashi da yammacin kasar, ta dangana daga birnin Drean na lardin El Tarf a gabas mai nisa, zuwa birnin Raml Souk mai iyaka da kasar Tunisiya.

Yayin bikin kaddamar da sashen karshe na wannan katafaren aiki a birnin El Tarf, firaministan Aljeriya Aymen Benabderrahmane ya jinjinawa muhimmin matsayin wannan aiki, wanda ya ce zai saukaka zirga-zirgar matafiya, ta bunkasa hada-hadar tattalin arziki tsakanin al’ummun Aljeriya da na Tunisiya.

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Benabderrahmane ya kuma yabi ingancin aikin hanyar, yana mai cewa, injiniyoyin kasar Aljeriya, da ’yan kwadago da suka shiga aka dama da su a aikin, sun samu karin kwarewa da sanin makamar aiki.

Yayin bikin kaddamarwar, mataimakin babban manajan kamfanin CITIC a kasar Aljeriya Qi Shujie, ya ce injiniyoyin kasar Sin sun fuskanci manyan kalubale yayin da suke gudanar da aikin, ciki har da bukatar gudanar da ciko mai tarin yawa, da matsalar zaftarewar kasa, tun fara aikin ginin kilomita 84 na shekarar 2017, amma duk da haka, sun kai ga kammala aikin a kan lokaci.

Bugu da kari, a wajen taron manema labarai da aka yi a yau Litinin, Wang ya kuma maida martani game da harin da aka kai wa wasu injiniyoyin kasar Sin dake tashar jiragen ruwa ta Gwadar a kasar Pakistan, yana mai cewa, kasar Sin na matukar Allah wadai da irin wannan harin ta’addanci, ta kuma bukaci Pakistan da ta yanke hukunci mai tsanani kan wadanda suka aikata wannan ta’asa, tare kuma da daukar matakan da suka wajaba, don tabbatar da tsaron mutanen Sin dake wajen. (Saminu Alhassan, Murtala Zhang)

Aljeriya
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
Za A Bude Bikin Baje Kolin Cinikayyar Hidima Na 2023 A Satumba

Za A Bude Bikin Baje Kolin Cinikayyar Hidima Na 2023 A Satumba

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.