ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?

by Sulaiman and El-Zaharadeen Umar
1 hour ago
Katsina

Noma na ɗaya daga cikin manyan sana’o’i ko mu ce ayyuka da mafiyawan al’umma jihar Katsina suka yi dogara da shi a matsayin hanya ta bunƙasa tattalin arziki da samar da cimaka.

To, sai dai, harkar noma ta gamo da babban ciwo wanda har gobe ake neman maganin sa domin a samu a warware ta yadda arziki zai cigaba da wanzuwa a tsakanin al’umma.

Ita ma jihar Katsina ta kasance wani ɓangare da ake tinƙaho da shi, wajen samar da kaso mai yawa a fannin noma shekara da shekaru.

ADVERTISEMENT

Sakamakon wancan cuta da ta kama harkar noma ta sanya hannun agogo ya koma baya, wanda yanzu haka gwamnati ta dukufa ba dare ba rana wajen ganin an dawo da martabar noma ta hanyar yin sa yadda ya kamata.

Tun kafin zuwan damina gwamnatin jihar Katsina ƙarƙashin jagorancin Malam Dikko Umar Radda ta ayyana kudirin ta na bunƙasa harkokin noma ta fannoni daban-daban.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Wa Manoma 2,930 Buhun Taki 11,720 A Abuja

Ku Gaggauta Fara Yin Shuka A Kakar Bana: Saƙon Hukumar NiMet Ga Manoma

Misalin haka shi ne, mun ga yadda aka fara da manoman rani, inda aka raba masu kayayyakin aikin noma wasu kyauta wasu kuma da kuɗi ƴan ƙalilan domin dai a dawo da martabar noma a jihar Katsina da ta shiga wani hali yau da rai gobe a mace…

A wannan karon an rabawa manoma kayayyakin aikin gona da yawa kuma na zamani da suka haɗa da takin zamani da na’uran huɗa (Power Tllers) ta zamani da kayan samar da ruwa ta hanyar haske rana da irin shuka da sauran su.

Dalilin samar da waɗannan ƙananan taraktoci na zamani shine yadda ɓarayin daji suka raba al’umma da shanun su, ta inda yanzu ganin shanu a wasu yankunan da ke fama da matsalolin tsaro ya zama abin mamaki.

Gwamna Raɗɗa ya ƙara da cewa samar da waɗannan ‘Power Tllers’ zai maye gurbin shanun da aka raba sakamakon hare-haren wuce gona da iri da ƴan bindiga suka riƙa kaiwa suna sace shanun al’umma.

Kazalika an baiwa manoman damina takin zamani akan farashi mai rahusa a ya yin da ake sayar da shi a kasuwa akan naira N50,00 kowane buhu amma ita gwamnati tana sayar da shi akan naira dubu ashirin da biyar.

Sannan ya ɗauki matakai na ganin cewa sai wanda yake manomi kuma ya nuna sha’awar yin noma sannan zai amfana da wannan tallafi na ragin kuɗin taki, kuma ita gwamnati ke ɗaukar nauyin kai duk inda al’umma za su karɓa.

Wannan gagarumin ragi da gwamnatin jihar Katsina ta ɓullo da shi zai taimaka wajen wahalhalun da manoma ke sha kafin samun takin zamani a kowace shekara.

Sannan kamar yadda rahotanni suka bayyana, an samar da wannan taki zamani da wuri sakamakon sauran shekarun baya da sai damina ta yi nisa sannan ake fara rabon takin zamani kuma mai rabo ke samu marar rabo dai kallo

To, sai dai duk wannan shiri da gwamnatin jihar Katsina da tarayya da kuma su kan su manoman da suka yi, ba za a samu nasarar samar da wadataccen abinci ba ta hanyar noma sai idan an samu yin noman yadda aka saba yi a baya sakamakon matsalolin tsaro da suka addabi wasu yankuna karkara.

Wato dai matsalar tsaro da ake fama da ita a wasu yankunan jihar Katsina inda kuma nan ne ginshikin yin noma a jihar har yanzu tana cigaba da maida hannun agogo baya a ƙoƙarin gwamnati na ganin an samu damar yin noma.

Duk lokacin da damina ta sauka ana fama da ƴan bindiga waɗanda suke ƙaƙabawa al’umma haraji idan har suna san yin noma a garuruwan su, sannan babu tabbas idan sun biya kuɗin za a bari su yi noman yadda ya kamata ko kuma su amfana da abinda suka noma.

Abubuwa biyu suke addabar harkokin noma a jihar Katsina, na farko dai tsadar kayan noma da kuma matsalolin ɓarayin daji, to, yanzu gwamnati ta yi huɓɓasa wajen samar da kayayyakin aikin gona ta hanya mai sauki.

Tambayar da kowa ke yi yanzu dai ita ce, wannan shiri da aka yi ko manoma a jihar Katsina za su amfana da ta, domin wancan matsala ta ɓarayin daji tana nan zaune da ƙafafuwanta babu inda ta je, gashi kuma manoma sun yi shiri fiye da kowane lokaci, shin ya a zata kaya ke nan.?

Bayan wancan ƙoƙari na gwamnatin jihar Katsina, ita ma gwamnatin tarayya ta yi na ta huɓɓasa ta inda ta yi gagarumin taron ƙaddamar raba takin zamani na arewa maso yamma a jihar Katsina, kuma wannan taki kyauta ne ba sayarwa ba ake yi na ga manema.

Gwamnatin shugaba Tinubu ƙarƙashin shirin sabinta fata (Renewed Hope) ta hanyar asusun bunƙasa noma na Nijeriya an raba buhun taki 100,800 ga manoma dubu 25,200 a yankin arewa maso yamma.

Wannan taki kamar yadda gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umar Raɗɗa ya bayyana kyauta ne ga manoma, kuma ɗaya daga cikin shirye-shiryen shugaban ƙasa ne na tallafawa harkar noma da manoma a Nijeriya

Haka kuma gwamnan jihar Katsina ɗin ya ƙara da cewa za su sanya ido su tabbatar takin zamanin ya kai inda ake so, ya kai, ta hanyar sa ido akan waɗanda aka ɗorawa alhakin tafiyar da wannan shiri.

Raɗɗa ya bayyana cewa wannan shiri na bada takin zamani kyauta an yi shi ne domin manoma na gaskiya wanda za a sanya ido don ganin abin ya kai gare su, ba tare da an karkatar da shi ba.

Dangane da ƙoƙarin gwamnatin tarayya na samar da takin zamani gwamna Raɗɗa ya ce jihar Katsina kawai ta samu buhu 20,160 wanda zata rabawa manoma 5,040 a ƙarƙashin shirin inganta harkokin noma a Nijeriya

Haka kuma ya bayyana wannan yunkuri na shugaban ƙasa a matsayin wani namijin ƙoƙari na farfaɗo da darajar noma musamman a arewacin Nijeriya da take da daɗaɗan tarihi a ɓangaren noma

To, sai dai kamar yadda masu sharhi akan al’amuran yau da kullum suka bayyana shi ne, yanzu matsalar manoma guda biyu ce, wato matsalar tsadar taki da kuma matsalolin ɓarayin daji wanda ake buƙatar kawo ƙarshen rashin tsaro fiye da komi a wannan lokaci.

Shin ina ƙaƙarin da gwamnatoci ke cewa suna yi akan sha’anin tsaro,? A iya cewa da yawan manoma ba su ganshi ba, domin matsalar na cigaba da ƙara zama ƙarfen ƙafa ga manoma da sauran al’umma. To yanzu ina mafita?

Ita dai wannan matsalar tsaron idan za a iya tunawa tuni ta raba da yawan al’umma daga garuruwan su, inda aka samu sasanshi ne tsakanin al’umma da ɓarayin daji sun fara komawa garuruwan su domin fuskantar wannan damina.

To, sai dai akwai wuraren da babu yadda za a yi al’umma su koma saboda yadda matsalar ta yi muni so sai, daman dai fatan da ake da shi shi ne, ganin an yi sasanshi kuma an fara ganin alfanun abin a wasu wurare yasa aka yi fatan cewa daminar bana za a yi noma so sai yadda ya kamata.

Daga yankunan da ake yin noma so sai a jihar Katsina yanzu haka an yanke masu sadarwa saboda matsalar tsaro sannan an hana su zuba fetur a cikin jarkoki wanda hakan na shafar yadda suke  tafiyar da  sha’anin noman na bana.

Kamar yadda aka bayyana gwamnatin tarayya da ta jihar Katsina sun rabawa manoma kayan aiki ciki harda ƙaramar tarakta ta noma mai amfani da man fetur wanda yanzu samar da man fetur ɗin domin yin amfani zai kasance wani babban ƙalubale ga manoma.

A wani sabon yunkuri da aka ce gwamnatoci na yi domin ganin an dawo da zaman lafiya a yankunan da ke fama da matsanancin rashin tsaro wanda zai baiwa manoman yin noma ba tare da wata fargaba ba shi ne karin jami’an tsaro a jihar Katsina

Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umar Raɗɗa ya ce ya daɗe bai ga ƙarin jami’an tsaron da gwamnatin tarayya ta turo jihar Katsina ba kamar a wannan lokacin ba da suka haɗa da sojoji da ƴan sanda da jami’an hukumar DSS da sauran jami’an tsaro

A cewar sa, yana fatan wannan yunkuri zai taimaka wajen ganin an samu nasarar murkushe wannan matsala da taki ci yaƙi cinye wa shekara da shekaru wanda kuma ta yi sanadiyar lakume rayuka da dukiyoyi da ba a san adadin su ba.

Yanzu gwamna Raɗɗa na cigaba da tattaunawa da ɓangarori daban-daban domin laluɓo hanyar da za a magance wannan matsala, abin jira a gani shi ne, irin tasirin da wannan yunkuri na baya baya nan zai yi akan wannan iftila’i na ɓarayin daji masu satar jama’a da hana nona.

Katsina
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Daga 1930 Zuwa 2026: Yadda Aka Buga Wasa Na Dubu Ɗaya A Gasar Kofin Duniya
  • Sulaiman
    Wakilin Sin: Kar A Bari Sabon Nau’in Ra’ayin Nuna Karfin Soja Ya Haifar Da Karin Tasiri
  • Sulaiman
    CDC Ta Afirka Ta Yaba Da Goyon Bayan Da Sin Ta Bayar Da Hadin Gwiwa Mai Karfi Wajen Yaki Da Ebola
  • Sulaiman
    Firaministan Guinea Ya Yabi Kasar Sin Bisa Shawarwarin Da Ta Gabatar
Katsina
El-Zaharadeen Umar
+ posts Bio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mutum 1,000 Daga Jam’iyyar ADC Sun Koma PDP A Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Tinubu Ya Amince Da Ɗaukar Ma’aikatan Gandun Daji 1,000 Domin Matsalolin Tsaro A Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Matsalar Tsaro:Yadda Sabbin Matakan Gwamnati Ke Shafar Walwalar Al’ummar Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

MASU ALAKA

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Wa Manoma 2,930 Buhun Taki 11,720 A Abuja

June 27, 2026
Katsina
Noma Da Kiwo

Ku Gaggauta Fara Yin Shuka A Kakar Bana: Saƙon Hukumar NiMet Ga Manoma

June 27, 2026
Katsina
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Fara Aikin Gina Mayankar Zamani A Garin Jos

June 26, 2026
Next Post
Wakilin Sin: Kar A Bari Sabon Nau’in Ra’ayin Nuna Karfin Soja Ya Haifar Da Karin Tasiri

Wakilin Sin: Kar A Bari Sabon Nau'in Ra'ayin Nuna Karfin Soja Ya Haifar Da Karin Tasiri

LABARAI MASU NASABA

Kofin Duniya

Daga 1930 Zuwa 2026: Yadda Aka Buga Wasa Na Dubu Ɗaya A Gasar Kofin Duniya

June 27, 2026
Wakilin Sin: Kar A Bari Sabon Nau’in Ra’ayin Nuna Karfin Soja Ya Haifar Da Karin Tasiri

Wakilin Sin: Kar A Bari Sabon Nau’in Ra’ayin Nuna Karfin Soja Ya Haifar Da Karin Tasiri

June 27, 2026
Manoma Sun Nemi Tinubu Ya Kara Yawan Tallafin Noma 

Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?

June 27, 2026
CDC Ta Afirka Ta Yaba Da Goyon Bayan Da Sin Ta Bayar Da Hadin Gwiwa Mai Karfi Wajen Yaki Da Ebola

CDC Ta Afirka Ta Yaba Da Goyon Bayan Da Sin Ta Bayar Da Hadin Gwiwa Mai Karfi Wajen Yaki Da Ebola

June 27, 2026
Firaministan Guinea Ya Yabi Kasar Sin Bisa Shawarwarin Da Ta Gabatar

Firaministan Guinea Ya Yabi Kasar Sin Bisa Shawarwarin Da Ta Gabatar

June 27, 2026
Zaben 2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Bayyana Shirinsu Yayin Da INEC Ta Fitar Da Jawalin Zabe

2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Yi Maraba Da Hukuncin Kotu Kan Dakatar Da Jadawalin INEC

June 27, 2026
ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya

ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya

June 27, 2026
TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

June 27, 2026
Magoya Bayan Pantami Sun Zargi Ana Musgunawa Gombawa Motors A Gombe

Magoya Bayan Pantami Sun Zargi Ana Musgunawa Gombawa Motors A Gombe

June 27, 2026
Babu Wani Saɓani Tsakanin Osimhen Da Lookman – Ndidi

Babu Wani Saɓani Tsakanin Osimhen Da Lookman – Ndidi

June 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.