A jiya Juma’a, zaunanen wakilin kasar Sin a Majalisar Dinkin Duniya, Fu Cong, ya halarci taron babban zauren Majalisar na tunawa da “ranar kundin Majalisar Dinkin Duniya”, inda ya ce, dole ne gamayyar kasa da kasa su yi kokarin kare sakamakon yakin duniya na biyu, kuma kar a bari sabon nau’in ra’ayin nuna karfin soja ya bazu, tare da haifar da karin tasiri a duniya.
Fu Cong ya kara da cewa, kasar Sin, bisa matsayinta na kasar da ta fara sanya hannu kan kundin Majalisar Dinkin Duniya, za ta ci gaba da daukar takamaiman matakai don cika alkawarinta na kare kundin Majalisar, da kokarin samar da gudunmowa ga yunkurin gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya.
Kana a wajen taron kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya game da batun kasar Congo Kinshasa, Fu Cong ya kalubalanci bangarori masu ruwa da tsaki da su tsagaita bude wuta a yankin gabashin kasar nan take. Ya ce, ya kamata kasashe daban-daban su bi dokar hana shigar da makamai cikin harabar kasar Congo Kinshasa, da cika alkawuran da suka dauka na ba da taimako wajen tabbatar da tsagaita wuta a kasar, yayin da a sa’i daya, ya kamata a girmama ikon mulkin kai, da ‘yancin kai, da kiyaye martabar yankin kasar ta Congo Kinshasa. Ban da haka, Fu ya kara da cewa, kasar Sin da kasashen Afirka, ciki har da Congo Kinshasa, har kullum suna cikin al’umma mai makomar bai daya, da huldar cude-ni-in-cude-ka. Kuma kasar Sin na kokarin aiki tare da sauran kasashe, don samar da karin gudunmowa ga yunkurin dawo da kwanciyar hankali, da raya tattalin arziki a kasar Congo Kinshasa.
Ban da haka, yayin da kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya ke tantance batun kasar Sudan. A madadin gwamnatin kasar Sin, Fu Cong ya mika shawarwari guda 4 ga gamayyar kasa da kasa, wato a tabbatar da tsagaita bude wuta a kasar Sudan, da tinkarar mawuyacin halin da ake ciki ta fuskar jin kai, da kara kokarin sulhuntawa, gami da magance bazuwar yake-yake zuwa yankuna makwabta. (Bello Wang)














