Hukumar kandagarki da yaki da annobar cututtuka ta Afirka (Africa CDC) a jiya Jumma’a ta yaba da hadin gwiwar da ta yi da kasar Sin wajen goyon bayan kokarin Afirka na shawo kan barkewar cutar Ebola.
Darakta janar na CDC ta Afirka, Jean Kaseya, ya yi wannan tsokaci bayan wata ganawa da babban jakadan Sin a kungiyar Tarayyar Afirka (AU), Jiang Feng, a hedikwatar kungiyar da ke Addis Ababa, babban birnin Habasha.
A yayin ganawar, jami’an biyu sun sanya hannu kan takardar shaidar mika tallafin gaggawa na dala miliyan 2 na kasar Sin domin karfafa kokarin Afirka kan yaki da cutar Ebola, kamar yadda Kaseya ya bayyana cikin wata sanarwa da ya fitar jiya Jumma’a ta shafin X wanda aka fi sani da Twitter a da.
Shugaban CDC ta Afirkar ya kuma yaba da “goyon baya da hadin gwiwa mai karfi na kasar Sin a kan lokaci” game da kokarin da nahiyar Afirka ke yi wajen yaki da cutar ta Ebola. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)














