Gwamnan Jihar Ribas, Siminalayi Fubara, ya musanta jita-jitar cewa ya fice daga jam’iyyar APC zuwa jam’iyyar NDC.
Fubara, ya bayyana haka ne yayin duba sabon aikin Babban Asibiti da kuma asibitin masu taɓin hankali da aka gyara a yankin Rumuigbo da ke ƙaramar hukumar Obiakpor a Jihar Ribas.
Ya ce har yanzu shi mamba ne na jam’iyyar APC, inda ya ja hankalin mutane da su daina yaɗa labaran ƙarya a kafafen sada zumunta.
Gwamnan ya kuma bayyana farin cikinsa kan kammala ayyukan asibitocin biyu, yana cewa an gina su ne domin inganta harkar lafiya saboda al’ummar yankin.
Fubara ya ce gwamnati ta yanke shawarar gina Babban Asibitin ne bayan gano cewa mazauna yankin ba su da asibiti a kusa da su face Asibitin Koyarwa na Jami’ar Fatakwal, wanda ke da nisa da yankin.
Ya bayyana ayyukan a matsayin cika alƙawuran da gwamnatinsa ta ɗauka a baya.















Discussion about this post