Ma’aikatar kula da albarkatun ruwa ta kasar Sin ta bayyana a jiya Talata cewa, ya zuwa karshen shekarar 2025, an sada kashi 96 cikin 100 na yankunan karkarar kasar Sin da ruwan famfo.Zuwa karshen shekarar da ta gabata, manyan ayyukan samar da ruwa sun karade kashi 71 cikin 100 na al’ummar karkara, yayin da kashi 72 cikin 100 na gundumomi suka rungumi tsarin gudanarwa na bai-daya na matakin gunduma wajen samar da ruwa a karkara, kamar yadda ma’aikatar ta bayyana a wani taron manema labarai.
Zuwa karshen shekarar 2025, kasar Sin tana da kusan ayyukan samar da ruwa a karkara miliyan 3.82, wadanda suka kafa tsarin samar da ruwa ga mazauna karkara miliyan 850. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)














Discussion about this post