ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, June 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Harajin Trump: Kaikayi Ya Koma Kan Mashekiya

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 months ago
Trump

Haramta kare-karen harajin kwastam da kotun kolin Amurka ta yi ga gwamnatin shugaba Trump kwanan nan, ta haifar da zafafan sharhohi daga masana shari’a da tattalin arziki, da masu lura da manufofin kasashen waje wadanda ke ganin hukuncin ya zarce batun gyara kuren nuna karfin iko a baibai.

Lamarin yana nuna damuwa mai zurfi, ba kawai game da tsarin gudanarwa bisa doka ba har ma da sha’anin huldar kasar a fagen kasa da kasa musamman kan abin da ya shafi cinikayya.

Hausawa kan ce, “idan mutum ya ce zai ba ka riga ka duba ta wuyarsa”, akwai kasashe da dama wadanda Amurka ke musu katsalandan a harkokinsu na cikin gida game da wai ba su bin doka, inda take amfani da gaban-kai da babakere wajen tayar musu da zaune tsaye, sai dai watakila an rufe bakin tsanya yanzu tun da ga misali nan a kanta.

ADVERTISEMENT

Abokan hulda na duniya suna sa ido sosai kan yadda Amurka ke fassara da kuma aiwatar da nata dokokin, musamman a cikin harkokin kasuwanci. Shi ya sa soke wata babbar manufa kamar ta tsarin biyan haraji bisa hujjar kakabata ta haramtacciyar hanya, yana haifar da tambayoyi a kasashen waje game da dogaro da alkawurran da Amurka ta dauka a kawancenta.

Gwamnatocin kasashen waje da kasuwannin duniya suna la’akari da tsayayyun manufofin Amurka ne da aka kafa bisa doka, ke nan matakai da ayyukan da Amurka ke aiwatarwa da suka saba wa dokokin cikin gida, za su iya raunana amincinta a tattaunawar kasa da kasa. Idan ana daukar shugaban kasar a matsayin wanda yake karan-tsaye ko watsi da iyakokin doka na gida, hakan zai yi matukar tasiri a cikin mu’amala da abokan hulda, da abokan ciniki, da kuma cibiyoyin da suka hade mabambantan bangarori.

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Harba Taurarin Dan Adam 8 Zuwa Sararin Samaniya

Mujallar Qiushi Za Ta Buga Muhimmin Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Ciyar Da Ilimi, Fasaha Da Kwararru Gaba Tare”

Babu makawa, hukuncin kotun kolin zai sake fasalin harkokin kasuwanci a duniya, duk da wata dokar zartaswa ta karin haraji da kaso 15 cikin dari da shugaba Trump ya sake rattaba hannu a kai, jim kadan da ayyana hukuncin. Kasashen da harajin ya shafa na iya sake tantance dabarunsu a yanzu, yayin da wasu kuma ke kallon hukuncin kotu a matsayin wata alama dake nuna cewa cibiyoyin hukuma a Amurka na da karfin dakile yin gaban-kai wanda ta wata fuskar kuma, hakan na da muhimmanci ga ba da tabbaci ga tsarin tattalin arzikin duniya.

Gwamnatin Trump ta kakaba kare-karen haraji marasa kan gado wanda wani shugaba bai taba yi ba a kasar da nufin wai cike gibin ciniki, amma maimakon hakan, sai gibin ya zama wagege, daga bisani kuma aka soke haramtattun kare-karen harajin, abin da gwamnatin ta shuka wa kasashe ya koma mata, lamarin da ke nuna kaikayi ya koma kan mashekiya! (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Trump
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Ta Harba Taurarin Dan Adam 8 Zuwa Sararin Samaniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin
Trump
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Kasar Sin Ta Harba Taurarin Dan Adam 8 Zuwa Sararin Samaniya
  • Sulaiman
    Mujallar Qiushi Za Ta Buga Muhimmin Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Ciyar Da Ilimi, Fasaha Da Kwararru Gaba Tare”
  • Sulaiman
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata
  • Sulaiman
    Ɗan Kwankwaso Ya Zama Mataimakin Ɗan Takarar Gwamnan NDC A Zaɓen Kano na 2027

MASU ALAKA

Kasar Sin Ta Harba Taurarin Dan Adam 8 Zuwa Sararin Samaniya
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Taurarin Dan Adam 8 Zuwa Sararin Samaniya

June 15, 2026
Mujallar Qiushi Za Ta Buga Muhimmin Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Ciyar Da Ilimi, Fasaha Da Kwararru Gaba Tare”
Daga Birnin Sin

Mujallar Qiushi Za Ta Buga Muhimmin Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Ciyar Da Ilimi, Fasaha Da Kwararru Gaba Tare”

June 15, 2026
Dunkulewar Kasa Shi Ne Burin Bai Daya Na Jama’ar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan
Daga Birnin Sin

Dunkulewar Kasa Shi Ne Burin Bai Daya Na Jama’ar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan

June 15, 2026
Next Post
Binciken CGTN Kan Alakar Sin Da Jamus: Ana Hada Karfi Da Karfe Daga Nesa Da Samun Aminci Cikin Lokaci 

Binciken CGTN Kan Alakar Sin Da Jamus: Ana Hada Karfi Da Karfe Daga Nesa Da Samun Aminci Cikin Lokaci 

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Hauhawar Farashi Ya Kai Kashi 15.93 Cikin 1000 A Watan Mayu A Nijeriya – NBS

Hauhawar Farashi Ya Kai Kashi 15.93 Cikin 1000 A Watan Mayu A Nijeriya – NBS

June 16, 2026
Sojoji Sun Ceto Matar Tsohon Kakakin Hedikwatar Tsaro A Katsina

Sojoji Sun Ceto Matar Tsohon Kakakin Hedikwatar Tsaro A Katsina

June 16, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Hukuncin Kotu Kan Ba Da Umarnin Soke Rajistar ADC

June 16, 2026
Kasar Sin Ta Harba Taurarin Dan Adam 8 Zuwa Sararin Samaniya

Kasar Sin Ta Harba Taurarin Dan Adam 8 Zuwa Sararin Samaniya

June 15, 2026
Mujallar Qiushi Za Ta Buga Muhimmin Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Ciyar Da Ilimi, Fasaha Da Kwararru Gaba Tare”

Mujallar Qiushi Za Ta Buga Muhimmin Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Ciyar Da Ilimi, Fasaha Da Kwararru Gaba Tare”

June 15, 2026
Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

June 15, 2026
Ɗan Kwankwaso Ya Zama Mataimakin Ɗan Takarar Gwamnan NDC A Zaɓen Kano na 2027

Ɗan Kwankwaso Ya Zama Mataimakin Ɗan Takarar Gwamnan NDC A Zaɓen Kano na 2027

June 15, 2026
2023: Tinubu Ya Zaɓi Kashim Shettima A Matsayin Mataimaki

Shin Har Yanzu Shettima Ne Abokin Takarar Tinubu?

June 15, 2026
Dunkulewar Kasa Shi Ne Burin Bai Daya Na Jama’ar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan

Dunkulewar Kasa Shi Ne Burin Bai Daya Na Jama’ar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan

June 15, 2026
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili

Mariya Mahmoud: Aiki A karkashin Jagorancin Wike

June 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.