ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Harin Maiduguri: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Saƙon Trump A Kan Tinubu

by Sadiq
3 months ago
Tinubu

Fadar Shugaban Ƙasa ta ce saƙon da ya karaɗe kafafen sada zumunta, wanda ke iƙirarin cewa Shugaban Amurka Donald Trump ya soki Shugaba Bola Tinubu kan hare-haren Maiduguri, ba gaskiya ba ne.

Mai bai wa Shugaban Ƙasa shawara kan harkokin yaɗa labarai, Sunday Dare, ya bayyana sakon a matsayin “ƙarya!!!” a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na X ranar Talata.

  • Gwamnonin Arewa Sun Yi Allah-wadai Da Hare-haren Ƙunar Baƙin Wake A Maiduguri
  • Manyan Ma’aunan Tattalin Arzikin Sin Sun Karu Daga Janairu Zuwa Fabrairu

Ya kuma wallafa hoton saƙon domin gargaɗin jama’a kan yaɗa labaran ƙarya.

ADVERTISEMENT

A cikin saƙon an bayyana cewa Trump ya zargi Tinubu da gazawa wajen magance matsalar tsaro a Arewa maso Gabas, tare da sukar tafiyarsa zuwa Birtaniya a lokacin da hare-haren a ƙasar.

Haka kuma saƙon ya ce Trump ya nemi Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, da ya umarci Tinubu ya dawo Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sai dai bincike ya nuna cewa Trump bai fitar da wannan bayani a shafukansa ba.

Wannan jita-jitar ta yaɗu ne a lokacin da ake cikin damuwa bayan hare-haren Maiduguri.

Da yammacin ranar Litinin, wasu da ake zargi ‘yan ƙunar baƙin wake ne sun kai hare-hare a wurare daban-daban na birnin, ciki har da wuraren da jama’a ke taruwa.

‘Yansanda sun ce aƙalla mutane 23 sun mutu, yayin da sama da 100 suka jikkata.

Hare-haren sun biyo bayan wani harin da aka kai wani sansanin sojoji a yankin Ajilari.

Shugaba Tinubu ya bayyana hare-haren a matsayin “abin takaici matuƙa”, yana mai ɗora laifi kan ƙungiyoyin ta’addanci da ke fuskantar matsin lamba daga dakarun Nijeriya.

Ya jajanta wa iyalan waɗanda suka rasu, ya kuma tausaya wa waɗanda suka jikkata, tare da tabbatar da cewa gwamnati za ta ci gaba da ƙoƙarin tabbatar da tsaro.

Haka kuma ya umarci shugabannin tsaro su koma Maiduguri domin jagorantar ayyukan tsaro, yana mai cewa Nijeriya ba za ta yarda ta’addanci ya yi tasiri ba.

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Dalilin Da Ya Sa Sin Ta Samu Ci Gaban Tattalin Arziki Mai Kyau A Watanni 2 Na Farkon Bana

Dalilin Da Ya Sa Sin Ta Samu Ci Gaban Tattalin Arziki Mai Kyau A Watanni 2 Na Farkon Bana

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.