Mamban ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS kuma mataimakin firaministan kasar Sin He Lifeng ya halarci taron ministocin cinikayya na kungiyar hadin gwiwar tattalin arzikin kasashen Asiya da Pasifik (APEC) a birnin Suzhou na kasar Sin.
Cikin jawabin da ya gabatar, He Lifeng ya ce yayin da duniya ke fuskantar sauye-sauye cikin sauri irin wadanda ba a taba gani ba cikin karni, ta hanyar rungumar ka’idojin mutuntawa da girmama juna da hadin gwiwar moriyar juna ne kadai kasashe mambobin APEC za su iya samun wadata na bai daya da samun ci gaba mai karko da daidaiton da inganci.
Ya ce a shirye Sin take ta hada hannu da dukkan bangarori wajen karfafa tuntubar juna da tattaunawa kan bangarori masu tasowa da hada hannu wajen goyon bayan aiwatar da gyare-gyare a hukumar kula da cinikayya ta duniya da inganta dunkulewar tattalin arzikin yankin Asiya da Pasifik yadda ya kamata, da kara wa ci gaban tattalin arzikin yankin da na duniya kuzari, ta hanyar nasarorin da ake samu daga zamanantar da kasar Sin. (Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post