Hukumar Hisbah ta Jihar Kebbi ta kama wani mutum da ake zargi da boye kansa cikin jakar “Ghana Must-Go” a gidan wata matar aure da ke unguwar Badariya a Birnin Kebbi.
Daraktan Shari’a na hukumar, Sirajo Kamba, ne ya tabbatar da faruwar lamarin cikin wata sanarwa da aka fitar ranar Talata a Birnin Kebbi.
Kamba, ya ce mazauna yankin sun fara zargin wani abu bayan sun lura da zirga-zirgar mutane a gidan matar da misalin karfe 12:15 a dare ranar Litinin, 18 ga watan Mayu.
Daga nan ne suka sanar da jami’an Hisbah kan abin da suka zargi ya saɓa wa koyarwar addinin Musulunci.
Bayan samun rahoton, jami’an Hisbah suka garzaya gidan domin gudanar da bincike.
A cewar Kamba, matar ta fara musanta cewa akwai mutum a cikin gidan lokacin da jami’an suka nemi su bincika gidan.
Sai dai daga baya ta ba su damar yin binciken.
Yayin binciken ne jami’an suka gano mutumin da ake zargi boye cikin jakar “Ghana Must-Go”.
Kamba ya ce bincike ya nuna cewa akwai alaƙar soyayya tsakanin mutanen biyun.
Ya ƙara da cewa dukkaninsu sun amsa zargin da ake musu, kuma za a gurfanar da su a kotu bisa tanade-tanaden dokar Musulunci.















Discussion about this post