ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gidan Tarihi: Gadar Da Ke Hada Wayewar Sin Da Afirka

by Sulaiman and CGTN Hausa
2 weeks ago
Tarihi

Ranar 18 ga watan Mayun kowace shekara ita ce “Ranar Gidan Tarihi ta Duniya”. Taken ranar ta bana shi ne “Gidan Tarihi: Gadar Da ke Hada Duniya”, wanda ke jaddada cewa gidan tarihi ba kawai ma’adanar abubuwan da suka gabata ba ne, har ma “gada” ce da ke hada al’adu daban-daban da kuma inganta cudanya tsakanin al’ummomi. Idan muka kalli nahiyar Afirka, za mu ga cewa gidajen tarihi da ke wasu kasashen nahiyar, ciki har da Morroco, Kenya, da Senegal, tamkar “gada” ce da ke bayyana ma’anar cudanyar al’ummu da musayar al’adu a tsakanin Sin da kasashen Afirka.

A cikin Gidan Tarihi na Ibn Battuta da ke birnin Tangiers da ke arewacin kasar Morroco, akwai samfurin jirgin ruwa na zamanin daular Yuan ta Sin da kwafin littafin “Tafiya ta Ibn Battuta”, wadanda ke nuna abubuwan da dan tafiya na kasar a karni na 14 ya gani a kasar Sin mai nisa, wato “Jirgin ruwan Sin kamar fada ce a kan teku”, “Tashar jiragen ruwa ta birnin Quanzhou cike da dubban jiragen ruwa, kasuwancin birnin Guangzhou ba ya hutawa dare da rana, kuma Hangzhou kamar lambun duniya”. Mai bayanin gidan tarihin ya ce yawancin yaran Morroco sun fara sanin Sin ne daga wajen Ibn Battuta. Har wa yau, a gidan tarihi na kasa na Kenya, an ajiye fasassun tangaran da yawa da suka fito daga kasar Sin. Alal hakika, a wuraren Lamu, Malindi na Kenya da Kilwa na Tanzaniya, masu binciken kayan tarihi sun gano kayayyakin fadi-ka-mutu da yawa da suka fito daga kasar Sin.

Wadannan “alamomin Sin” da suka warwatsu a kasashen Afirka, hakika sun shaida “musayar wayewa” tsakanin Sin da Afirka, wadanda suke bayyana mana cewa, huldar Sin da Afirka ba wai ta fara ne da hadin gwiwar tattalin arziki na zamani ba, tana samun tushe ne daga tsarin ciniki ta tekun Indiya da aka yi tun shekaru daruruwa da suka wuce. Dangane da dangantakar Sin da Afirka, gidan tarihi ya zama tamkar “madubi”, wanda ke nuna abubuwan da suka faru a baya da yiwuwar nan gaba.

ADVERTISEMENT

Gidan tarihi shi ne mai rikon gaskiyar tarihi. Lokacin da muka kalli kwano mai kyalli na zamanin daular Ming a gidan tarihin kayayyakin tangaran na birnin Alkahira na kasar Masar, abin da muke gani ba fasahar hada kayayyakin fadi-ka-mutu kawai ba ne, har ma da yadda aka yi musaya da wanzar da lumana a tsakanin Sin da Afirka a shekaru 600 da suka wuce. Kamar yadda Farfesa Farouk, masanin tarihi na Jami’ar Alexandria ta kasar Masar ya ce, ayarin jiragen ruwan babban mai tafiya a kan teku na Sin Zheng He na zamanin daular Ming ya bar wa Afirka “tangaran da siliki da shayi da kuma musayar al’adu”. A ganinsa, babban bambanci tsakanin Zheng He da ayarin jiragen ruwan Turawan mulkin mallaka na baya shi ne manufar tafiyarsu. “Zheng He bai zo da mulkin mallaka ba. Wannan tafiyar wanzar da lumana har yanzu yana da tasiri a kasashen Afirka da yawa.” Wadannan kayan tarihi sun kuma karyata maganar wai “Sin tana kafa sabon salon mulkin mallaka a Afirka”.

Gidan tarihi shi ne kuma mai sa kaimin musayar wayewar kai. Wadannan kayayyakin tangaran na kasar Sin da aka gano a gabar tekun gabashin Afirka, daga baya sun hade cikin al’adun gine-ginen Afirka. A wasu tsofaffin gidaje na garin Lamu da ke Kenya, har yanzu ana iya ganin farantin tangaran na kasar Sin da aka saka a cikin bango. Ba su kasance kayan abinci kawai ba, sun zama wani bangare na fasahar gine-ginen Afirka daga baya. Wannan tasiri a hankali shi ne babbar darajar “musayar al’adu”.Gidan tarihi har wa yau shi ne tushen hadin gwiwa a nan gaba.

LABARAI MASU NASABA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

Gidan tarihin wayewar bakaken fata na Senegal wanda gwamnatin kasar Sin ta taimaka wajen gina shi, yanzu haka ba wai alamar al’adu ce ta yammacin Afirka kadai ba, har ma da sabon dandalin musayar al’adu a tsakanin Sin da Afirka. Kamar yadda daraktan gidan tarihin Hamady Bocoum ya ce: “Musayar al’adu tsakanin Sin da Afirka ba ta fara daga yau ba.” A zamanin da ake samun bunkasuwar sassa daban daban, gidajen tarihi za su taimakawa matasan Sin da Afirka su fahimci zurfin ma’anar shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya”.

Lokacin da muke kallon wadannan fasassun tangaran daga kasar Sin a gidan tarihi na birnin Nairobi, ko karanta littafin tafiya na Ibn Battuta a cikin gidan tarihinsa, a hakika muna shiga cikin cudanyar al’adu da ta ketare lokaci da sarari. Wannan, watakila ita ce kyauta mafi daraja da gidan tarihi ke ba mu: ganin tarihi, fahimtar abin da ya gabata, don mu kara dagewa wajen tafiya tare zuwa nan gaba.

Tarihi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Tarihi
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

MASU ALAKA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

May 29, 2026
Next Post
Kotu Ta Yanke Wa Tsohon Ministan Wutar Lantarki Saleh Mamman Hukuncin Shekaru 75 A Gidan Yari

EFCC Ta Kama Tsohon Ministan Wutar Lantarki Saleh Mamman Da Ya Tsere

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.