ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar Shari’a Ta Kano Ta Hukunta Alƙalai Da Ma’aikata Kan Laifukan Rashin Ɗa’a

by Sulaiman
2 months ago

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

Hukumar Kula da Ayyukan Shari’a ta Jihar Kano, ta ɗauki matakan ladabtarwa kan wasu jami’an shari’a da ma’aikata bisa laifukan rashin da’a, tana mai jaddada kudurinta na tabbatar da “tsari, gaskiya da riƙon amana a cikin ɓangaren shari’a.”

An cimma waɗannan matsayai ne a taro na 89 na hukumar da aka gudanar a ranar 16 ga Afrilu, 2026, kamar yadda kakakin hukumar, Baba Jibo Ibrahim, ya bayyana a wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar.Ibrahim ya ce hukumar ta amince da shawarwarin Kwamitin Karɓar Korafe-korafe na Jama’a na Shari’a dangane da ƙorafe-ƙorafe daban-daban da aka bincika.

Daga cikin waɗanda abin ya shafa akwai Mahmud Ahmed, jami’in sufuri na Babbar Kotun Kano, wanda aka samu da aikata abubuwan da suka wuce aikinsa, yin barazana ga jama’a, da amfani da sunan ɓangaren shari’a wajen tsoratar da mutane. An ba shi gargaɗi mai tsanani tare da umarnin ya takaita kansa ga aikinsa kawai.

A wani lamari, Mallam Salisu Buhari Mandawari, alƙalin Kotun Shari’ar Musulunci ta Ƙoli a Rogo, an same shi da aikata abubuwan da suka haɗa da nema da karɓar cin hanci, da kuma kasa rubuta bayanan shari’a yadda ya kamata. Hukumar ta rage masa matsayi da darajoji biyu, tare da dakatar da shi daga aikin shari’a na akalla shekaru uku, sannan zai riƙa karɓar rabin albashi.

Haka kuma, Alkali Umar Sunusi Danbaba na Kotun Shari’ar Musulunci ta Filin Hoki, an hukunta shi bayan an same shi da son zuciya, rashin rubuta bayanan shari’a yadda ya kamata, da kuma rashin kyakkyawan kula da kuɗi. Sabida haka, an dakatar da shi daga aikin shari’a na akalla shekaru uku, tare da karɓar rabin albashi na shekara guda.

Hukumar ta kuma gano cewa, Abdulbari Ado (Magatakardan Kuɗi) da Umar Abdulhamid (Magatakardan Gudanarwa) suna da hannu wajen karɓar cin hanci a wani lamari da ya shafi Kotun Shari’ar Musulunci a Rogo. Dukkaninsu an rage musu matsayi da darajoji biyu, an sanya su kan rabin albashi na shekara guda, tare da gargadin su da su guji sake aikata laifi.

A wani lamari daban, Sabiu Adam Inusa, Magatakardan Kuɗi a Kotun Shari’ar Musulunci ta Gwarzo, an same shi da bayar da rasit mai kura-kurai. Duk da an ɗauki lamarin a matsayin kuskure, hukumar ta ba shi gargaɗi tare da cire shi daga muƙaminsa na Magatakardan Kuɗi.


Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Aikin Maɗaciya A Jikin Ɗan’adam

Aikin Maɗaciya A Jikin Ɗan’adam

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.