Hukumar Kula da Ayyukan Shari’a ta Jihar Kano, ta ɗauki matakan ladabtarwa kan wasu jami’an shari’a da ma’aikata bisa laifukan rashin da’a, tana mai jaddada kudurinta na tabbatar da “tsari, gaskiya da riƙon amana a cikin ɓangaren shari’a.”
An cimma waɗannan matsayai ne a taro na 89 na hukumar da aka gudanar a ranar 16 ga Afrilu, 2026, kamar yadda kakakin hukumar, Baba Jibo Ibrahim, ya bayyana a wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar.Ibrahim ya ce hukumar ta amince da shawarwarin Kwamitin Karɓar Korafe-korafe na Jama’a na Shari’a dangane da ƙorafe-ƙorafe daban-daban da aka bincika.
Daga cikin waɗanda abin ya shafa akwai Mahmud Ahmed, jami’in sufuri na Babbar Kotun Kano, wanda aka samu da aikata abubuwan da suka wuce aikinsa, yin barazana ga jama’a, da amfani da sunan ɓangaren shari’a wajen tsoratar da mutane. An ba shi gargaɗi mai tsanani tare da umarnin ya takaita kansa ga aikinsa kawai.
A wani lamari, Mallam Salisu Buhari Mandawari, alƙalin Kotun Shari’ar Musulunci ta Ƙoli a Rogo, an same shi da aikata abubuwan da suka haɗa da nema da karɓar cin hanci, da kuma kasa rubuta bayanan shari’a yadda ya kamata. Hukumar ta rage masa matsayi da darajoji biyu, tare da dakatar da shi daga aikin shari’a na akalla shekaru uku, sannan zai riƙa karɓar rabin albashi.
Haka kuma, Alkali Umar Sunusi Danbaba na Kotun Shari’ar Musulunci ta Filin Hoki, an hukunta shi bayan an same shi da son zuciya, rashin rubuta bayanan shari’a yadda ya kamata, da kuma rashin kyakkyawan kula da kuɗi. Sabida haka, an dakatar da shi daga aikin shari’a na akalla shekaru uku, tare da karɓar rabin albashi na shekara guda.
Hukumar ta kuma gano cewa, Abdulbari Ado (Magatakardan Kuɗi) da Umar Abdulhamid (Magatakardan Gudanarwa) suna da hannu wajen karɓar cin hanci a wani lamari da ya shafi Kotun Shari’ar Musulunci a Rogo. Dukkaninsu an rage musu matsayi da darajoji biyu, an sanya su kan rabin albashi na shekara guda, tare da gargadin su da su guji sake aikata laifi.
A wani lamari daban, Sabiu Adam Inusa, Magatakardan Kuɗi a Kotun Shari’ar Musulunci ta Gwarzo, an same shi da bayar da rasit mai kura-kurai. Duk da an ɗauki lamarin a matsayin kuskure, hukumar ta ba shi gargaɗi tare da cire shi daga muƙaminsa na Magatakardan Kuɗi.















Discussion about this post