ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar Shari’a Ta Kano Ta Hukunta Alƙalai Da Ma’aikata Kan Laifukan Rashin Ɗa’a

by Sulaiman
2 months ago

LABARAI MASU NASABA

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

Hukumar Kula da Ayyukan Shari’a ta Jihar Kano, ta ɗauki matakan ladabtarwa kan wasu jami’an shari’a da ma’aikata bisa laifukan rashin da’a, tana mai jaddada kudurinta na tabbatar da “tsari, gaskiya da riƙon amana a cikin ɓangaren shari’a.”

An cimma waɗannan matsayai ne a taro na 89 na hukumar da aka gudanar a ranar 16 ga Afrilu, 2026, kamar yadda kakakin hukumar, Baba Jibo Ibrahim, ya bayyana a wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar.Ibrahim ya ce hukumar ta amince da shawarwarin Kwamitin Karɓar Korafe-korafe na Jama’a na Shari’a dangane da ƙorafe-ƙorafe daban-daban da aka bincika.

Daga cikin waɗanda abin ya shafa akwai Mahmud Ahmed, jami’in sufuri na Babbar Kotun Kano, wanda aka samu da aikata abubuwan da suka wuce aikinsa, yin barazana ga jama’a, da amfani da sunan ɓangaren shari’a wajen tsoratar da mutane. An ba shi gargaɗi mai tsanani tare da umarnin ya takaita kansa ga aikinsa kawai.

A wani lamari, Mallam Salisu Buhari Mandawari, alƙalin Kotun Shari’ar Musulunci ta Ƙoli a Rogo, an same shi da aikata abubuwan da suka haɗa da nema da karɓar cin hanci, da kuma kasa rubuta bayanan shari’a yadda ya kamata. Hukumar ta rage masa matsayi da darajoji biyu, tare da dakatar da shi daga aikin shari’a na akalla shekaru uku, sannan zai riƙa karɓar rabin albashi.

Haka kuma, Alkali Umar Sunusi Danbaba na Kotun Shari’ar Musulunci ta Filin Hoki, an hukunta shi bayan an same shi da son zuciya, rashin rubuta bayanan shari’a yadda ya kamata, da kuma rashin kyakkyawan kula da kuɗi. Sabida haka, an dakatar da shi daga aikin shari’a na akalla shekaru uku, tare da karɓar rabin albashi na shekara guda.

Hukumar ta kuma gano cewa, Abdulbari Ado (Magatakardan Kuɗi) da Umar Abdulhamid (Magatakardan Gudanarwa) suna da hannu wajen karɓar cin hanci a wani lamari da ya shafi Kotun Shari’ar Musulunci a Rogo. Dukkaninsu an rage musu matsayi da darajoji biyu, an sanya su kan rabin albashi na shekara guda, tare da gargadin su da su guji sake aikata laifi.

A wani lamari daban, Sabiu Adam Inusa, Magatakardan Kuɗi a Kotun Shari’ar Musulunci ta Gwarzo, an same shi da bayar da rasit mai kura-kurai. Duk da an ɗauki lamarin a matsayin kuskure, hukumar ta ba shi gargaɗi tare da cire shi daga muƙaminsa na Magatakardan Kuɗi.


Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • Sulaiman
    ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya

June 3, 2026
Next Post
Aikin Maɗaciya A Jikin Ɗan’adam

Aikin Maɗaciya A Jikin Ɗan’adam

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.