Sanata Ali Ndume mai wakiltar Borno ta Kudu ya bayyana dalilin da ya sa yake goyon bayan ƙirƙirar ‘yansandan jihohi a Nijeriya, yana mai cewa adadin ‘yansandan da ƙasar ke da su bai isa ya magance matsalar tsaro ba.
Da yake magana a wata hira da ya yi a gidan talabijin na Arise a ranar Laraba, Ndume ya ce Nijeriya mai yawan jama’a sama da miliyan 200 na buƙatar aƙalla ‘yansanda miliyan ɗaya.
Kalaman nasa na zuwa ne bayan Majalisar Dattawa ta amince da ƙudirin dokar ƙirƙirar ‘yansandan jihohi domin taimakawa wajen magance matsalar tsaro a faɗin ƙasar.
A cewarsa, adadin ‘yansandan Nijeriya na yanzu ya yi ƙasa da ƙa’idar da ƙasashen duniya suka tanada.
Ndume ya ce ba zai yiwu a samu tsaro a ƙasa mai girman Nijeriya ba idan rundunar ‘yansanda tana ƙarƙashin jagoranci guda ɗaya na Sufeto Janar na ‘Yansanda daga cibiyar tarayya.
Ya bayyana cewa tsarin ‘yansandan jihohi zai fi tasiri, inda kowace jiha za ta samu rundunarta ƙarƙashin ikon gwamna, wanda shi ne babban jami’in tsaro na jihar.
Ya ƙara da cewa ƙirƙirar ‘yansandan jihohi zai taimaka wajen inganta tsaro da kuma ƙara tasirin ayyukan jami’an tsaro a faɗin Nijeriya.














