Shugaban rikon kwarya na kungiyar Tarayyar Afirka AU, kuma shugaban kasar Burundi Evariste Ndayishimiye, ya ce duk da yake yanayin siyasa da tattalin arzikin duniya na ci gaba da canzawa, Sin da kasashen Afirka su kasance abokan tafiya tare bisa gaskiya da amincewar juna, kuma Sin na iya taka muhimmiyar rawa wajen zamanantar da nahiyar Afirka.
Shugaba Ndayishimiye ya bayyana hakan ne a kwanan nan a Gitega, babban birnin siyasar kasar Burundi, yayin zantawa ta musamman da wakilan kamfanin dillancin labarai na Xinhua, inda ya ce a bana ake cika shekaru 70 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin Sin da nahiyar Afirka.
Daga ranar 1 ga watan Mayun bana, Sin ta fara aiwatar da manufar soke haraji gaba daya ga kasashe 53 na Afirka da ke da alakar diplomasiyya da ita. Game da hakan, Ndayishimiye ya bayyana cewa, wannan matakin da Sin ta dauka ya samar da babbar dama ga kasashen Afirka, ciki har da Burundi.
Ya ce manufar soke harajin na iya taimakawa kasarsa wajen kara samun kudin shiga ta bangaren fitar da kayayyaki, da samar da ayyukan yi mai dorewa ga matasa, da kuma ciyar da bunkasar masana’antar sarrafa kayayyaki na Afirka gaba. (Amina Xu)














