Tsohon Shugaban Rundunar Sojin Nijeriya, Tukur Yusuf Buratai, ya bayyana cewa yana da yaƙinin hukumomin tsaro na ƙasar na da ƙarfin gano waɗanda suka sace ɗalibai da malamai a Jihar Oyo.
Buratai ya bayyana hakan ne a wata hira da aka yi da shi a gidan talabijin na TVC, inda ya ce bai yarda cewa maharan sun fi ƙarfin jami’an tsaro ba.
Ya ce idan jami’an tsaro na iya bibiya da gano wasu ‘yan ƙasa da masu amfani da kafafen sada zumunta, to ya kamata su iya gano ƙungiyoyin da ke aikata laifukan garkuwa da mutane.
Ya kuma ce gano masu laifi kaɗai bai wadatar ba, sai an ci gaba da inganta ƙwarewa da ƙarfin hukumomin tsaro a kai a kai.
Buratai ya buƙaci a ƙara yawan sojoji da ‘yansanda domin ƙarfafa yaƙi da matsalolin tsaro a ƙasar.
Ya kuma bayyana cewa Nijeriya na da rundunoni na musamman da aka horar domin ayyukan ceto, musamman wajen kuɓutar da waɗanda aka sace, amma dole a yi aiki cikin taka-tsan-tsan don guje wa cutar da waɗanda aka yi garkuwa da su.
Wannan na zuwa ne bayan sace ɗalibai da malamai a Oyo a ranar 15 ga watan Mayu, lamarin da ya haifar da zanga-zanga da kuma ƙarin kira ga gwamnati da ta ɗauki matakin gaggawa wajen magance matsalolin tsaro.















Discussion about this post