Tsohon Mataimakin Gwamnan Jihar Bauchi, Arc. Audu Sule Katagum, ya rasu yana da shekaru 69 a duniya. Marigayin ya riƙe muƙamin mataimakin gwamna tsakanin 2018 zuwa 2019 a zamanin tsohon Gwamna Mohammed Abdullahi Abubakar.
Rasuwar tasa ta faru ne da sanyin safiyar ranar Asabar, kamar yadda Shamsuddeen Lukman Abubakar, mai ba tsohon gwamna shawara kan harkokin yaɗa labarai na zamani, ya tabbatar a cikin wata sanarwa.
A cewar sanarwar, marigayin ya yi rayuwa mai cike da hidima ga al’umma, da jihar Bauchi da ƙasa baki ɗaya, inda ya riƙe sarautar Wazirin Katagum kuma fitaccen ɗan siyasavda ya bayar da gudummawa wajen kawo ga ci gaba.
Za a sanar da cikakken tsarin jana’izarsa nan gaba, yayin da ake yi masa addu’ar Allah Ya gafarta masa.














Discussion about this post