Hukumar gudanarwar Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBU) da ke Bauchi ta janye izinin bada fili wa ƙungiyar ɗalibai na ɓangaren Ɗarikar Tijjaniyya wato ‘Tijjaniyya Muslim Students Association of Nigeria’ (TIMSAN) a cikin harabar jami’ar da ke Gubi domin gina masallaci.
Jami’ar ta kuma sanar da shirinta na sake yin garambawul ga tsarin gudanar da harƙoƙin addini ta hanyar tabbatar da cewa dukkanin ɓangarorin Musulunci da ke cikin jami’ar su na da wakilci a cikin Majalisar Shura da kuma shugabancin ƙungiyar ɗalibai musulmai ‘Muslim Students’ Society of Nigeria’ (MSSN) reshen jami’ar.
Daraktan yaɗa labarai da hulɗa da Jama’a na jami’ar, Alhaji Zailani Bappa, shi ne ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai da ya yi a sakatariyar ‘yan jarida da ke Bauchi a ranar Laraba.
Ya ce taron ya mayar da hankali ne kan cece-ku-cen da suka biyo bayan bai wa reshen TIMSAN na ATBU fili domin gina masallaci.
Takaddamar ta samo asali ne bayan da babban limamin jami’ar, Farfesa Mansur Isa Yelwa, tare da mataimakinsa, suka yi murabus a ranar Juma’a, 26 ga Yunin 2026, domin nuna rashin amincewarsu da matakin jami’ar na bai wa TIMSAN fili mai girman ƙafa 100 by 50 domin gina masallaci don gudanar da ayyukansu na addini.
Sai dai wakilinmu ya tabbatar da cewa Farfesa Mansur ya janye murabus ɗinsa kuma ya koma bakin aikinsa a matsayin Babban Limamin jami’ar.
A baya dai, jami’ar ta bayyana cewa manufar bai wa TIMSAN filin ita ce domin ba ƙungiyar damar gina masallaci da za ta gudanar da ayyukan ibadarta, ciki har da Wazifa, bisa tanadin kundin tsarin mulkin ƙasa da ke bai wa kowa ‘yancin gudanar da addininsa cikin ‘yanci. Lamarin kuma ya samo asali tun daga hana ‘yan darikar damar yin wazifa a masallatan da suke ƙarƙashin kungiyar MSSN.
Bappa ya ce sanarwar murabus ɗin Limamin ya jawo martani daga sassa daban-daban na ƙasa da ma ƙasashen waje, tare da haifar da damuwar tsaro a jami’ar da sauran manyan makarantun gaba da sakandare.
Ya bayyana cewa mahukuntan jami’ar sun ga ya dace su fayyace gaskiyar abin da ya faru, yana mai cewa matakin bai wa TIMSAN fili ya biyo bayan ƙin amincewar Majalisar Shura da membobin TIMSAN su gudanar da ayyukansu na addini a babban masallacin jami’ar.
A cewarsa, wannan rikici ya sa hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta shiga tsakani, inda ta kira taron masu ruwa da tsaki domin samar da mafita cikin lumana. Ya ce taron, wanda aka gudanar ranar Talata, 30 ga Yunin 2026, a shalkwatar DSS da ke Bauchi, ya samu halartar wakilan mahukuntan jami’ar, Majalisar Shura, reshen MSSN na ATBU da kuma reshen TIMSAN na ATBU.
Bappa ya ce mahalarta taron sun amince cewa daga yanzu za a bai wa dukkan ɓangarorin Musulunci da ke jami’ar damar gudanar da ayyukansu na addini a lokutan da za a ware musu a masallatan jami’ar. Ya ƙara da cewa an kuma yanke shawarar cewa mahukuntan jami’ar ne za su riƙa naɗa babban limami da mataimakansa, tare da tabbatar da cewa dukkan harƙoƙin addini a harabar jami’ar suna gudana bisa ƙa’idoji da dokokin jami’ar.
Ya yaba wa DSS bisa saurin shiga tsakani da kuma ƙoƙarin da ta yi wajen dawo da zaman lafiya.
Ya ce, “Mahukuntan Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa suna yaba wa shugabancin DSS a Bauchi saboda saurin shiga tsakani, kuma suna tabbatar wa dukkan masu ruwa da tsaki cewa za a aiwatar da dukkan shawarwarin da aka cimma domin tabbatar da dorewar zaman lafiya da haɗin kai a harabar jami’ar.”
Bappa ya kuma bayyana cewa dukkan shawarwarin da aka cimma a taron an amince da su tare da sanya hannu a kansu daga dukkan bangarorin da suka halarta.
Hakazalika, ya tabbatar da cewa nan ba da jimawa ba hukumar gudanarwar jami’ar za ta sanar da wasu ƙarin matakai da suka shafi shugabancin babban masallacin jami’ar da sauran harkokin Musulmi, domin ƙarfafa zaman lafiya, haɗin kai da kwanciyar hankali a cikin jami’ar.














