ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
2 days ago
ATBU

Hukumar gudanarwar Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBU) da ke Bauchi ta janye izinin bada fili wa ƙungiyar ɗalibai na ɓangaren Ɗarikar Tijjaniyya wato ‘Tijjaniyya Muslim Students Association of Nigeria’ (TIMSAN) a cikin harabar jami’ar da ke Gubi domin gina masallaci.

Jami’ar ta kuma sanar da shirinta na sake yin garambawul ga tsarin gudanar da harƙoƙin addini ta hanyar tabbatar da cewa dukkanin ɓangarorin Musulunci da ke cikin jami’ar su na da wakilci a cikin Majalisar Shura da kuma shugabancin ƙungiyar ɗalibai musulmai ‘Muslim Students’ Society of Nigeria’ (MSSN) reshen jami’ar.

Daraktan yaɗa labarai da hulɗa da Jama’a na jami’ar, Alhaji Zailani Bappa, shi ne ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai da ya yi a sakatariyar ‘yan jarida da ke Bauchi a ranar Laraba.

ADVERTISEMENT

Ya ce taron ya mayar da hankali ne kan cece-ku-cen da suka biyo bayan bai wa reshen TIMSAN na ATBU fili domin gina masallaci.

Takaddamar ta samo asali ne bayan da babban limamin jami’ar, Farfesa Mansur Isa Yelwa, tare da mataimakinsa, suka yi murabus a ranar Juma’a, 26 ga Yunin 2026, domin nuna rashin amincewarsu da matakin jami’ar na bai wa TIMSAN fili mai girman ƙafa 100 by 50 domin gina masallaci don gudanar da ayyukansu na addini.

LABARAI MASU NASABA

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

Kano Pillars Ta Naɗa Mataimakin Kocin Super Eagles, Daniel Ogunmodede A Matsayin Sabon Kocinta

Sai dai wakilinmu ya tabbatar da cewa Farfesa Mansur ya janye murabus ɗinsa kuma ya koma bakin aikinsa a matsayin Babban Limamin jami’ar.

A baya dai, jami’ar ta bayyana cewa manufar bai wa TIMSAN filin ita ce domin ba ƙungiyar damar gina masallaci da za ta gudanar da ayyukan ibadarta, ciki har da Wazifa, bisa tanadin kundin tsarin mulkin ƙasa da ke bai wa kowa ‘yancin gudanar da addininsa cikin ‘yanci. Lamarin kuma ya samo asali tun daga hana ‘yan darikar damar yin wazifa a masallatan da suke ƙarƙashin kungiyar MSSN.

Bappa ya ce sanarwar murabus ɗin Limamin ya jawo martani daga sassa daban-daban na ƙasa da ma ƙasashen waje, tare da haifar da damuwar tsaro a jami’ar da sauran manyan makarantun gaba da sakandare.

Ya bayyana cewa mahukuntan jami’ar sun ga ya dace su fayyace gaskiyar abin da ya faru, yana mai cewa matakin bai wa TIMSAN fili ya biyo bayan ƙin amincewar Majalisar Shura da membobin TIMSAN su gudanar da ayyukansu na addini a babban masallacin jami’ar.

A cewarsa, wannan rikici ya sa hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta shiga tsakani, inda ta kira taron masu ruwa da tsaki domin samar da mafita cikin lumana. Ya ce taron, wanda aka gudanar ranar Talata, 30 ga Yunin 2026, a shalkwatar DSS da ke Bauchi, ya samu halartar wakilan mahukuntan jami’ar, Majalisar Shura, reshen MSSN na ATBU da kuma reshen TIMSAN na ATBU.

Bappa ya ce mahalarta taron sun amince cewa daga yanzu za a bai wa dukkan ɓangarorin Musulunci da ke jami’ar damar gudanar da ayyukansu na addini a lokutan da za a ware musu a masallatan jami’ar. Ya ƙara da cewa an kuma yanke shawarar cewa mahukuntan jami’ar ne za su riƙa naɗa babban limami da mataimakansa, tare da tabbatar da cewa dukkan harƙoƙin addini a harabar jami’ar suna gudana bisa ƙa’idoji da dokokin jami’ar.

Ya yaba wa DSS bisa saurin shiga tsakani da kuma ƙoƙarin da ta yi wajen dawo da zaman lafiya.

Ya ce, “Mahukuntan Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa suna yaba wa shugabancin DSS a Bauchi saboda saurin shiga tsakani, kuma suna tabbatar wa dukkan masu ruwa da tsaki cewa za a aiwatar da dukkan shawarwarin da aka cimma domin tabbatar da dorewar zaman lafiya da haɗin kai a harabar jami’ar.”

Bappa ya kuma bayyana cewa dukkan shawarwarin da aka cimma a taron an amince da su tare da sanya hannu a kansu daga dukkan bangarorin da suka halarta.

Hakazalika, ya tabbatar da cewa nan ba da jimawa ba hukumar gudanarwar jami’ar za ta sanar da wasu ƙarin matakai da suka shafi shugabancin babban masallacin jami’ar da sauran harkokin Musulmi, domin ƙarfafa zaman lafiya, haɗin kai da kwanciyar hankali a cikin jami’ar.

ATBU
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran
  • Sulaiman
    Sin Ta Soki Abin Da Amurka Da Tarayyar Turai Ke Kira Da Wai ‘Damuwa Kan Sabuwar Dokar Kabilu’
  • Sulaiman
    CGTN Ta Gudanar Da Nazari Kan Yadda Jama’Ar Duniya Ke Kallon Amurka
  • Sulaiman
    An Kaddamar Da Taron Kasa Da Kasa Na 2026 Kan Tattalin Arzikin Dijital A Beijing
ATBU
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC
Manyan Labarai

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026
Kano Pillars Ta Naɗa Mataimakin Kocin Super Eagles, Daniel Ogunmodede A Matsayin Sabon Kocinta
Manyan Labarai

Kano Pillars Ta Naɗa Mataimakin Kocin Super Eagles, Daniel Ogunmodede A Matsayin Sabon Kocinta

July 3, 2026
Gwamnan Kano Ya Buƙaci EFCC, ICPC Su Sa Ido Kan Rabon Tallafin Taki
Manyan Labarai

Gwamnan Kano Ya Buƙaci EFCC, ICPC Su Sa Ido Kan Rabon Tallafin Taki

July 3, 2026
Next Post
Kiristoci Ma Na Iya Shiga Cikin Shirin Auren Gata Na Kano – Hisbah

Kiristoci Ma Na Iya Shiga Cikin Shirin Auren Gata Na Kano - Hisbah

LABARAI MASU NASABA

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026
Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC

July 4, 2026
Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

July 4, 2026
Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

NPA Ta Ɗaura Ɗamarar Magance Matsalolin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.