ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
3 weeks ago
ATBU

Hukumar gudanarwar Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBU) da ke Bauchi ta janye izinin bada fili wa ƙungiyar ɗalibai na ɓangaren Ɗarikar Tijjaniyya wato ‘Tijjaniyya Muslim Students Association of Nigeria’ (TIMSAN) a cikin harabar jami’ar da ke Gubi domin gina masallaci.

Jami’ar ta kuma sanar da shirinta na sake yin garambawul ga tsarin gudanar da harƙoƙin addini ta hanyar tabbatar da cewa dukkanin ɓangarorin Musulunci da ke cikin jami’ar su na da wakilci a cikin Majalisar Shura da kuma shugabancin ƙungiyar ɗalibai musulmai ‘Muslim Students’ Society of Nigeria’ (MSSN) reshen jami’ar.

Daraktan yaɗa labarai da hulɗa da Jama’a na jami’ar, Alhaji Zailani Bappa, shi ne ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai da ya yi a sakatariyar ‘yan jarida da ke Bauchi a ranar Laraba.

ADVERTISEMENT

Ya ce taron ya mayar da hankali ne kan cece-ku-cen da suka biyo bayan bai wa reshen TIMSAN na ATBU fili domin gina masallaci.

Takaddamar ta samo asali ne bayan da babban limamin jami’ar, Farfesa Mansur Isa Yelwa, tare da mataimakinsa, suka yi murabus a ranar Juma’a, 26 ga Yunin 2026, domin nuna rashin amincewarsu da matakin jami’ar na bai wa TIMSAN fili mai girman ƙafa 100 by 50 domin gina masallaci don gudanar da ayyukansu na addini.

LABARAI MASU NASABA

Sana’ar Kilishi:Yadda Ta Bunkasa Daga Jihar Katsina Zuwa Wasu Sassan Nijeriya

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Sai dai wakilinmu ya tabbatar da cewa Farfesa Mansur ya janye murabus ɗinsa kuma ya koma bakin aikinsa a matsayin Babban Limamin jami’ar.

A baya dai, jami’ar ta bayyana cewa manufar bai wa TIMSAN filin ita ce domin ba ƙungiyar damar gina masallaci da za ta gudanar da ayyukan ibadarta, ciki har da Wazifa, bisa tanadin kundin tsarin mulkin ƙasa da ke bai wa kowa ‘yancin gudanar da addininsa cikin ‘yanci. Lamarin kuma ya samo asali tun daga hana ‘yan darikar damar yin wazifa a masallatan da suke ƙarƙashin kungiyar MSSN.

Bappa ya ce sanarwar murabus ɗin Limamin ya jawo martani daga sassa daban-daban na ƙasa da ma ƙasashen waje, tare da haifar da damuwar tsaro a jami’ar da sauran manyan makarantun gaba da sakandare.

Ya bayyana cewa mahukuntan jami’ar sun ga ya dace su fayyace gaskiyar abin da ya faru, yana mai cewa matakin bai wa TIMSAN fili ya biyo bayan ƙin amincewar Majalisar Shura da membobin TIMSAN su gudanar da ayyukansu na addini a babban masallacin jami’ar.

A cewarsa, wannan rikici ya sa hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta shiga tsakani, inda ta kira taron masu ruwa da tsaki domin samar da mafita cikin lumana. Ya ce taron, wanda aka gudanar ranar Talata, 30 ga Yunin 2026, a shalkwatar DSS da ke Bauchi, ya samu halartar wakilan mahukuntan jami’ar, Majalisar Shura, reshen MSSN na ATBU da kuma reshen TIMSAN na ATBU.

Bappa ya ce mahalarta taron sun amince cewa daga yanzu za a bai wa dukkan ɓangarorin Musulunci da ke jami’ar damar gudanar da ayyukansu na addini a lokutan da za a ware musu a masallatan jami’ar. Ya ƙara da cewa an kuma yanke shawarar cewa mahukuntan jami’ar ne za su riƙa naɗa babban limami da mataimakansa, tare da tabbatar da cewa dukkan harƙoƙin addini a harabar jami’ar suna gudana bisa ƙa’idoji da dokokin jami’ar.

Ya yaba wa DSS bisa saurin shiga tsakani da kuma ƙoƙarin da ta yi wajen dawo da zaman lafiya.

Ya ce, “Mahukuntan Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa suna yaba wa shugabancin DSS a Bauchi saboda saurin shiga tsakani, kuma suna tabbatar wa dukkan masu ruwa da tsaki cewa za a aiwatar da dukkan shawarwarin da aka cimma domin tabbatar da dorewar zaman lafiya da haɗin kai a harabar jami’ar.”

Bappa ya kuma bayyana cewa dukkan shawarwarin da aka cimma a taron an amince da su tare da sanya hannu a kansu daga dukkan bangarorin da suka halarta.

Hakazalika, ya tabbatar da cewa nan ba da jimawa ba hukumar gudanarwar jami’ar za ta sanar da wasu ƙarin matakai da suka shafi shugabancin babban masallacin jami’ar da sauran harkokin Musulmi, domin ƙarfafa zaman lafiya, haɗin kai da kwanciyar hankali a cikin jami’ar.

ATBU
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya
  • Sulaiman
    Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya
  • Sulaiman
    Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150
  • Sulaiman
    Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari
ATBU
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Harbe Mai Unguwa Har Lahira A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ba Mu Sayar Wa Dangote Da Reshen Jami’ar SAZU Na Yuli Ba-Gwamnatin Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

MASU ALAKA

Sana’ar Kilishi:Yadda Ta Bunkasa Daga Jihar Katsina Zuwa Wasu Sassan Nijeriya
Manyan Labarai

Sana’ar Kilishi:Yadda Ta Bunkasa Daga Jihar Katsina Zuwa Wasu Sassan Nijeriya

July 24, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
Manyan Labarai

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 24, 2026
Wasikar Trump Ba Za Ta Taimaki Tinubu Ya Lashe Zaɓen 2027 Ba – ADC
Manyan Labarai

Wasikar Trump Ba Za Ta Taimaki Tinubu Ya Lashe Zaɓen 2027 Ba – ADC

July 23, 2026
Next Post
Kiristoci Ma Na Iya Shiga Cikin Shirin Auren Gata Na Kano – Hisbah

Kiristoci Ma Na Iya Shiga Cikin Shirin Auren Gata Na Kano - Hisbah

LABARAI MASU NASABA

NNPP Za Ta Kwace Mulki A Jihar Imo – Kwankwaso

Jam’iyyar NDC Ta Shirya Tsaf Domin Kafa Gwamnati A 2027 —Kwankwaso

July 24, 2026
Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

July 24, 2026
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

July 24, 2026
Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026
Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

July 24, 2026
Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

July 24, 2026
NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci

NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci

July 24, 2026
Sin Tana Son More Damammakin Fasahar AI a Maimakon Babakere a Wannan Bangare Da Kasashen Yamma Suka Dade Suna Yi

Sin Tana Son More Damammakin Fasahar AI a Maimakon Babakere a Wannan Bangare Da Kasashen Yamma Suka Dade Suna Yi

July 24, 2026
Kwairanga Ya Kafa Tarihi A Shugabancin Hukumar Kula Da Kasuwar Hannun Jari Ta Nijeriya

Kwairanga Ya Kafa Tarihi A Shugabancin Hukumar Kula Da Kasuwar Hannun Jari Ta Nijeriya

July 24, 2026
Yadda Kotun Daukaka Kara Ta Kama Hanyar Cin Gashin Kanta

Yadda Kotun Daukaka Kara Ta Kama Hanyar Cin Gashin Kanta

July 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.