Ɗan Majalisar Dokokin Jihar Bauchi mai wakiltar mazaɓar Sakwa, Hon. Mohammad Wanzam, ya rasu da safiyar yau Lahadi.Kafin rasuwarsa, Hon. Wanzam shi ne shugaban kwamitin kasafin kuɗi (Appropriation) na majalisar dokokin jihar Bauchi, inda ya gudanar da ayyukansa cikin ƙwazo, jajircewa da sadaukarwa, kamar yadda majalisar ta ce.
Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Bauchi, Rt. Hon. Abubakar Y. Sulaiman, shi ne ya sanar da rasuwar ta ɗan majalisar a ranar Lahadi.
A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Kakakin Majalisar, Mukhtar Garba Kobi, ya fitar, Kakakin ya bayyana marigayin a matsayin jajirtacce wanda ya hidimta wa al’umma da mazaɓarsa da ma jihar Bauchi gwargwadon iyawarsa.
Sanarwar ta ce, “Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un. Cikin matsanancin alhini da cikakken mika wuya ga ƙaddarar Allah Maɗaukakin Sarki, ina sanar da rasuwar ɗan Majalisar Dokokin Jihar Bauchi mai wakiltar mazaɓar Sakwa, Hon. Mohammad Wanzam.”Sanarwar ta ƙara da cewa za a gudanar da sallar jana’izar marigayin a Masallacin Juma’a na Gwallaga da ke Bauchi a ranar Lahadi da ƙarfe 11:00 na safe.
Kakakin Majalisar ya yi addu’ar Allah Maɗaukakin Sarki Ya gafarta wa marigayin kura-kuransa, Ya karɓi ayyukansa na alheri, sannan Ya ba shi gidan Aljannatul Firdaus.















Discussion about this post