Ministan harkokin waje na kasar Iran Abbas Araqchi, ya bayyana a jiya Juma’a cewa, Iran tana godiya ga duk wata kasa dake iya ba ta taimako, musamman ma kasar Sin.
Mista Abbas ya fadi hakan ne yayin taron manema labaru da ya gudana a birnin New Delhi na kasar Indiya. A cewarsa, kasar Sin ta taba samar da taimako wajen maido da huldar diflomasiyya tsakanin kasar Iran da Saudiyya.
Kana akwai hulda mai kyau tsakanin Iran da Sin, ganin yadda Sin din ta kasance abokiyar kasar Iran ta hulda mai alaka da manyan tsare-tsare.
Ban da haka, bangaren Iran na sane cewa har kullum kasar Sin na da niyyar kirki. Saboda haka, kasar Iran ke farin cikin ganin yadda kasar Sin ke kokarin samar da damar daidaita rikicin da ake yi tsakaninta da Amurka ta hanyar diflomasiyya.
Har ila yau, jami’in na kasar Iran ya kara da cewa, har yanzu aikin da kasar Pakistan take yi na ingiza sulhu bai ci tura ba, amma ana cikin wani yanayi mai matukar wuya.
Kuma dalilin da ya sa haka, shi ne aikace-aikace marasa dacewa daga bangaren Amurka, da karancin amincewa da juna tsakanin bangarorin Iran da Amurka. (Bello Wang)















Discussion about this post